Aminiya:
2025-09-17@20:28:12 GMT

Gidauniyar Misilli ta mayar da yara 150 makaranta a Gombe

Published: 15th, September 2025 GMT

A cikin shekaru uku da kafuwarta, gidauniyar Misilli, ta mayar da yara 150 makarantar boko a Jihar Gombe, ciki har da mata 88 da maza 62, tare da ɗaukar nauyin kuɗaɗen karatunsu.

Wannan mataki ya taimaka wajen rage nauyin iyaye marasa hali, inda suka samu ’yancin zaɓar makarantun da ke kusa da su.

Ambaliya: NEDC ta raba wa mutum 2,200 kayan agaji a Yobe An yi wa zakarun wasan motsa jiki ruwan kuɗi a Akwa Ibom

Shirin AGILE ya tallafa wa gidauniyar da litattafai domin ƙarfafa wannan yunƙuri, lamarin da shugabar shirin a Gombe, Dokta Amina Haruna Abdul, ta yaba da shi tare da alƙawarin yin haɗin gwiwa.

Ita ma, Dokta Hauwa Yahaya Umar daga SUBEB, ta ce irin wannan haɗin gwiwa yana ƙara wa gwamnati ƙwarin gwiwa bunƙasa ilimi.

A nasa ɓangaren, Daraktan shirye-shirye a Ma’aikatar Ilimi, Dokta Kabir Musa, ya yaba da ƙoƙarin gidauniyar tare da kira da ta ci gaba da tallafa wa al’umma.

Daraktan ayyuka na gidauniyar, Malam Yusuf Hamza, ya bayyana cewa duk da cewa ayyukan sun fi karkata ga Karamar Hukumar Gombe, ana shirin faɗaɗa shi zuwa wasu yankuna.

Ya ce suna tallafawa a fannoni da dama, ciki har da lafiya, ruwan sha, samar da tiransufoma da fitilu, da kuma shirin saka fitilu masu hasken rana guda 20 a unguwanni.

A fannin ilimi kuwa, Yusuf, ya ce suna biyan kuɗin makaranta, samar wa ɗalibai kuɗin karatu a makarantun sakandare 72, da kuma biyan kuɗin JAMB.

Shugaban gidauniyar, Isma’ila Uba Misilli, wanda shi ne babban daraktan yaɗa labarai na gwamnan Gombe, ya gode wa masu ruwa da tsaki bisa gudunmawar da suka bayar.

Gidauniyar ta bai wa yara uku da suka fi nuna ƙwazo kekunan hawa, sannan aka bai wa sauran ɗalibai jakunkuna da kayan karatu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gidauniya Kayan Karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa