Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Published: 14th, September 2025 GMT
Liɓerpool ce mai riƙe da kofin kuma na 20 jimilla da ta lashe a kakar da ta wuce, iri ɗaya da yawan wanda Manchester United take da shi a tarihin gasar premier ta ƙasar Ingila.
Ga jerin ƙungiyoyin da suka ci ribar kasuwancin sayen ƴan ƙwallo da waɗanda suka yi hasara a cikin ƙungiyoyin da suke buga gasar Premier League ta bana.
LIVERPOOL
Ƙungiyar ce kan gaba a yawan kashe kuɗi wajen sayen ƴan ƙwallo a bana, wadda karo biyu ta ɗauki ƴan wasa a matakin mafi tsada a kakar nan. Ta fara da sayen matashin ɗan wasa Florian Wirtz kan fam miliyan 115, sannan ta ɗauki Aleɗander Isak kan fam miliyan 125 ranar da za a rufe kasuwar.
Cikin ƴan ƙwallon da ta saye har da Jeremie Frimpong kan fam miliyan 30 da Milos Kerkez kan fam miliyan 40 sai kuma Hugo Eketike, ɗan Faransa, wanda ya koma ƙungiyar dafa Frankfurt. Haka kuma Liɓerpool ta sayer da Luis Diaz da Darwin Nunez da Jarell Ƙuansah daga ƙarshe ba ta samu damar sayen Marc Guehi daga Crystal Palace ba, bayan da Palace ɗin ta ce ba ta samu ɗaukar madadin Guehi ba.
ARSENAL
Arsenal ta fitar da maƙudan kuɗaɗe wajen sayen ƴan wasa da yawa, domin taimakawa Mikel Arteta a ƙoƙarin da yake na ganin ya lashe kofuna a bana, musamman Premier League, wadda rabonta da kofin kaka 22 kenan. Cikin ƴan wasan da ta ɗauka har da Viktor Gyokeres, wanda ya kawo matsalar rashin mai buga gurbin cin ƙwallaye, bayan da ke fama da jinya.
Haka kuma Arsenal ta sayi Eberechi Eze da Noni Madueke da Martin Zubimendi da Christian Norgaard da Cristhian Mosƙuera da kuma Piero Hincapie. Bugu da ƙari ƙungiyar ta London ta ɗauki mai tsaron raga Kepa Arrizabalaga, duk dai domin ta taka rawar gani a kakar nan, sannan Arteta ya ƙara lashe kofuna bayan FA Cup a kakarsa ta farko da kuma Community Shield.
NOTTINGHAM FOREST
Tuni ƙungiyar ta kori kocinta, Nuno Espirito Santo bayan rashin fahimtar juna da suke ci gaba da samu da daraktan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar, Edu Gaspar, Forest ta shiga kasuwa ta yi cefanen ƴan wasa don ganin ta yi abin kirki a kakar nan.
Sau biyu a ƙungiyar tana sayen ɗan wasa a matakin mafi tsada a tarhinta, bayan sayen Dan Ndoye da kuma Omari Hutchinson. Sannan ta kuma kashe fam miliyan 30 kuɗin sayen James McAtee, sai kuma Douglas Luiz da ya koma buga Premier League daga Juɓentus ta kuma ɗauki Nicolo Saɓona.
A ranar da za a rufe kasuwar cinikin ƴan ƙwallo ƙungiyar ta sake ɗaukar aron Oleksandr Zinchenko ta sayi Dilane Bakwa, sannan ta kuma yi nasarar riƙe ɗan wasan tawagar Ingila, Morgan Gibbs-White, bayan da Tottenham ta yi ƙoƙarin sayen ɗan ƙwallon.
Sai dai duk da haka akwai ƙungiyoyin da za a iya cewa asara suka yi a wannan kakar idan aka kalli yan wasan da suka sayer da kuma waɗanda suka saye kafin a rufe kasuwar
NEWCASTLE UNITED
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Newcastle United ta sayi ɗan wasan Brentford, Yoane Wissa da ɗan ƙwallon Stuttgart, Nick Woltemade, wadda ta fara da ɗaukar ɗan wasan Nottingham Forest, Anthony Elanga.
Sai dai kuma ba za a manta da batun Aleɗander Isak ba, wanda ya dage sai da ya bar ƙungiyar, har da ƙin buga mata wasannin atisayen tunkarar kakar bana da wasa biyu da ta buga a Premier League ta bana.
Kuma rashin Isak ya sa tana shan wahala wajen cin ƙwallaye, hakan ya sa ta yi zawarcin madadinsa daga ciki har da Hugo Ekitike da ya zaɓi Liɓerpool da Benjamin Sesko da ya koma Manchester United har da Joao Pedro da ya zaɓi Chelsea sai kuma Jorgen Strand Larsen, wanda Woɓes ta ƙi sayer da shi.
ASTON VILLA
Ita ma ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Aston Villa tana fatan yin gogayya cikin ƴan shidan farko a Premier League a kakar nan, amma ta ci karo da cikas kan dokar kashe kuɗi daidai samu. Duk da haka ta sayer da matashi, Jacob Ramsey, wanda magoya baya ba su ji daɗi ba.
Sai dai ƙungiyar ta ɗauki Harɓey Elliott daga Liɓerpool da kuma ɗan wasan Manchester United, Jadon Sancho, amma dai Villa ba ta samu yin cinikin da zai bata damar yin abin kirki ba, kenan sai abin da ta gani.
BRENTFORD
Bayan da Brentford ta rasa kociyanta, Thomas Frank da ya koma Tottenham ta kuma sayer da ƴan ƙwallo uku da ya haɗa da Bryan Mbeumo ga Manchester United, yayin da Norgaard ya koma Arsenal da kuma Newcastle da ta sayi Wissa. Sai dai ta sayo Dango Outtara daga Bournemouth kan fam miliyan 42.5, amma dai tana da jan aiki bayan rashin fitattun ƴan ƙwallonta uku a kakar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Wasa Firimiya Transfer kan fam miliyan ƙungiyar ta a kakar nan
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya kada kuri’ar nuna goyan baya ga wani kudiri da ya jaddada cewa shirin da Morocco ta gabatar kan Yammacin Sahara shi ne mafita ‘’mafi dacewa” ga yankin da ake takaddama a kai.
Kudirin ya nuna goyan bayan kasashe mambobin kwammitin ga shirin na Morocco, tare da bayyana cewa ikon masarautar kan yankin zai iya kasancewa mafita mafi dacewa.
Kan hakan ne kwamitin yaya kira ga Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres da wakilinsa na musamman kan wannan batu, Staffan de Mistura, da su gudanar da tattaunawa “bisa ga” wannan shirin don cimma yarjejeniya da kowa zai aminta da ita.
Aljeriya wacce ta ke kaddama da Morocco kan yankin ta kaurace kada kuri’an kan batun inda ta bayyana matukar adawarta da kudirin.
Jakadan Aljeriya, Amar Benjama, ya ce kudirin bai dace da burin mutanen Yammacin Sahara, wadanda kungiyar Polisario ke wakilta ba.
Kudurin da aka amince da shi a ranar Juma’a ya kuma tsawaita aikin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Yammacin Sahara (MINURSO) na tsawon shekara guda.
Shirin wanda Rabat ta gabatar a ranar 11 ga Afrilu, 2007, don mayar da martani ga kiran da Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi na samar da mafita ta siyasa game da yankin na yammacin Sahara.
Kudirin na yanzu ya tanadi samar da gwamnati da shugaban yankin, da majalisar dokoki wadda ta kunshi wakilan kabilun Sahrawi daban-daban da membobi da aka zaba ta hanyar zaben gama gari kai tsaye.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci