’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
Published: 15th, September 2025 GMT
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta shiga tsakani don sasanta rikicin da ya ɓarke tsakanin Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO).
Rikicin ya samo asali ne daga katse wutar lantarki da asibitin ya zargi KEDCO da yi, inda ya ce hakan ya kawo cikas ga ayyukan lafiya masu muhimmanci a asibitin, ciki har da zargin mutuwar marasa lafiya.
Sasantawar da Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya jagoranta ta biyo bayan zarge-zargen cewa katsewar wutar ta haddasa mutuwar wasu marasa lafiya da ke kan na’urar taimakon numfashi a asibitin.
Sai dai KEDCO ya musanta zargin a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, yana mai cewa asibitin na kokarin bata sunansa ne kawai.
A cewar mai magana da yawun ‘yan sanda na Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, an gudanar da taron sasancin ne a hedikwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai, inda aka zauna da Shugaban asibitin, Farfesa Abdulrahman Abba Sheshe, da Shugaban KEDCO, Abubakar Shuaibu Jimeta.
Taron ya mayar da hankali ne kan warware tankiyar da kuma dawo da wutar lantarki ga asibitin, wanda ke ya fuskanci matsaloli sakamakon katse wutar.
Sanarwar ta ce, “Bangarorin biyu sun nuna godiya ga matakin gaggawa da ‘yan sanda suka dauka. KEDCO ya amince da dawo da wutar lantarki nan take, alamar cewa rikicin ya zo karshe.”
Kiyawa ya kara da cewa, “Rundunar ‘Yan Sanda ta jaddada kudirinta na kare rayuka da dukiyoyi, tare da tabbatar da ci gaba da aiki ba tare da tangarda ba a bangaren kiwon lafiya.”
Sanarwar ta kuma ce kwamishinan ‘yan sanda ya yaba wa AKTH da KEDCO bisa hadin kai, tare da alkawarin ci gaba da goyon baya don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA