Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Published: 14th, September 2025 GMT
“Shawarar tsarin shugabancin duniya” ta zama kalmar da aka sha karanta a rahotannin kafofin watsa labaru na duniya cikin kwanakin baya. Shugabannin wasu kasashe da dama suna ganin cewa, wannan shawarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a yayin taron koli na SCO da aka gudanar a kwanan baya a birnin Tianjin, tana da muhimmiyar ma’ana a fannin warware matsalolin da suka shafi tsarin shugabancin duniya a yanzu.
A halin yanzu, sauyin karfi a tsakanin kasashe masu ci gaba da ma kasashe masu tasowa shi ne sauyi mafi girma da aka samu a sabon zamanin da muke ciki a fagen kasa da kasa, inda tarin kasashe masu tasowa suka bunkasa da sauri. To sai dai kuma tsarin duniya da ake bi a yanzu haka, bai nuna wani sauyi mai zurfi ba, kuma hakan ya haddasa rashin wakilci, da karfin fada-a-ji na kasashe masu tasowa.
Shawarar tsarin shugabancin duniya ta kunshi muhimman ra’ayoyi, irin su “zaman daidaito wajen mulkin kai”, da “kiyaye tsarin dokoki na kasashen duniya” da “aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori da dama” da dai sauransu, wadanda ke nufin kara fito da muryoyin kasashe masu tasowa a duniya. Saboda haka ne ma kasashe masu tasowa, suka fi mayar da martani kan shawarar. Kafafen yada labaran kasar Iran sun gabatar da sharhi dake cewa, “Al’ummun kasashe masu tasowa ba za su kasance ‘yan kallo kadai ba, maimakon haka za su himmatu wajen shiga ayyukan tsara makomarsu ta gaba.”
A cikin shekaru hudu da suka gabata, kasar Sin ta gabatar da shawarwari guda hudu na kasa da kasa da suka shafi ci gaba, da tsaro, da wayewar kai da ma shugabanci, wadanda suka ba da tabbaci ga duniyarmu da ke fama da tashin hankali. A nan gaba, duk wani canji da yanayin siyasar duniya zai samu, kasar Sin za ta ci gaba da kiyaye tsarin cudanyar kasashen duniya dake mayar da MDD a matsayin ginshikinsa, da dokokin kasa da kasa a matsayin tushensa. Za kuma ta yi aiki tare da bangarori daban daban, don ciyar da tsarin shugabancin duniya gaba yadda ya kamata, da inganta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil’adama, da kuma kokartawa wajen wanzar da zaman lafiya da ci gaban bil’adama. (Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tsarin shugabancin duniya kasashe masu tasowa
এছাড়াও পড়ুন:
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
“Ana kiransa da suna dokar binciken tntanet ta tsoratarwa, wadda kasashen da suka ci gaba da dama suka dade da yin watsi da ita. A karni na 21, ba za a iya tunanin cewa gwamnatin Nijeriya za ta tauye ‘yancin fadin albarkacin baki, wanda shi ne ginshikin mulkin dimokuradiyya.”
Atiku ya ce duk wata doka da ke take ‘yancin ‘yan kasa na yin tsokaci mai muhimmanci game da shugabanninsu ko a hanyoyin sadarwar zamani ko ta hanyar magana ba dimokuradiyya ba ce kuma kai tsaye take hakkokin Dan’adam ne.
“A cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata tun bayan da gwamnatin Tinubu ta fara daukan matakan da ke janyo kuncin tattalin arziki da yunwa da bakin ciki ga mutanen Nijeriya, mun shaida zanga-zanga da koke-koke daga ‘yan kasa da ba za su iya daukar mulkin rashin gaskiya ba. Duk da haka, maimakon sauraron ‘yan kasa sai gwamnatin ta zabi hanyar amfani da karfin hukumo da tsoratarwa wadda ta juya lamarin zuwa wani abu daban.
“Lallai abin bakin ciki ne na ganin ana take hakkin ‘yan kasa da kundin tsarin mulki ya tabbatar a lokacin da ya kamata dimokuradiyyarmu ta kasance mai bin tsari. Dole ne mu tunatar da gwamnatin Tinubu cewa babu gwamnati a lokacin da ta kasa kare ‘yancin ‘yan kasarta, komai karfinta kuwa. Yin haka abun ta da hankali ne kuma hakan yana nuna gazawar gwamnati a fili.”
Atiku ya ce tabbas gwamnati na da alhakin kula da doka da oda, babu ingantacciyar gwamnati da za ta harbi masu zanga-zangar lumana da harsashi mai rai ko ta boye a bayan dokoki tana musguna wa ‘yan kasa.
Ya ce rashin kulawar gwamnati Tinubu ga dokar kasa da kuma ci gaba da kin bin umarnin kotu sun zama shahararrun siffofinta mafiya suna a kasar nan a halin yanzu.
Tsohon mataimakin shugaban kasa ya kara da cewa tun farkon wannan gwamnati, kungiyar kare hakkin Dan’ada ta Amnesty ta soke wannan gwamnatin da take hakkin Dan’adam.
Ya ce haka ma wasu kungiyoyi masu muhimmanci kamar irinsu kungiyar ‘yan jaridu ta Nijeriya da kungiyar kare ajandar kafafen yada labarai sun yi korafi kan cin zarafin ‘yan jarida da ‘yan kasa ta hannun jami’an gwamnati.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA