A cewarsa, kudaden fansa da ake yawan ji ana biya yawanci iyalan wadanda abin ya shafa ko al’ummarsu ne ke tarawa.

 

Ya kuma bayyana cewa rahotanni sun nuna ’yan bindiga sun karɓi sama da Naira biliyan 2.5 a shekarar 2025 kadai, adadin da ya ce babu wata gwamnati da za ta iya ɗauka.

 

Masanin tsaron ya ce matsalar tsaro a Najeriya ta fi ƙarfin dabarun soja kaɗai, inda ya danganta ta da cin hanci da rashawa wanda ya kira “babban mai ba da damar ayyukan ta’addanci.

 

Ya yi gargadin cewa ya zama dole a guji yin zarge-zargen da ba su da tushe kan shugabannin da ke kan karagar mulki, yana mai tunatar da cewa irin wadannan maganganu an taba yi a kan gwamnatocin baya ma.

 

Yayin da yake bayani kan tsarin rundunar sojoji. Bukarti ya jaddada cewa shugaban kasa ne kadai ke da ikon bayar da umarnin daukar matakin soja. Ya ce gwamnoni, ministocin tsaro da ma mai ba da shawara kan harkokin tsaro ba su da wannan iko. A cewarsa, tsarin umarni daga shugaban kasa yake farawa zuwa Babban Hafsan Soja, sannan daga can zuwa kwamandojin filin daga.

 

A ƙarshe, Dr. Bukarti ya ce magance matsalolin tsaro a Najeriya na bukatar dogon lokaci, hadin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro da ’yan kasa, tare da tsaurara matakan yaki da cin hanci da rashawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin