Gwamnatin Tarayya za ta gurfanar da shugabannin Ansaru 2 a kotu
Published: 11th, September 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya za ta gurfanar da manyan shugabannin ƙungiyar ’yan ta’adda ta Ansaru a kotu a yau Alhamis.
Za a gurfanar da su ne a Babban Kotun Tarayya da ke Abuja.
Tinubu ya bayar da umarnin a sake karya farashin kayan abinci EFCC ta tsare Mele Kyari kan binciken matatun maiMutanen da za a gurfanar su ne Mahmud Muhammad Usman, wanda aka fi sani da Abu Bara’a, da mataimakinsa Abubakar Abba, wanda aka fi sani da Mahmud Al-Nigeri ko Mallam Mamuda.
Za su fuskanci tuhume-tuhume 32 da suka shafi ta’addanci.
Tuhuma ta farko ta ce, mutanen sun taimaka wajen tsara da jagorantar ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru tsakanin 2013 zuwa 2015.
An haramta ayyukan Ansaru a Najeriya kuma tana da alaƙa da Al-Qaeda.
Abu Bara’a wanda yake ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Okene a Jihar Kogi ne, yayin da Mahmud Al-Nigeri ya fito daga Ƙaramar Hukumar Daura ta Jihar Katsina.
An kama su ne yayin wani samame da hukumomin tsaro da na leƙen asiri suka gudanar tsakanin watan Mayu zuwa Yulin 2025.
Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan sha’anin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ne, ya bayyana kama su a ranar 16 ga watan Agusta, a Abuja.
Ana zargin Ansaru da kai hare-hare da sace mutane masu yawa a faɗin Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Ansaru Gurfanarwa Gwamnatin tarayya Ƙungiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.