Leadership News Hausa:
2025-11-02@08:41:08 GMT

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

Published: 11th, September 2025 GMT

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS ta ce, shugabannin sun samu horo na musamman a kan amfani da makamai, dabarun yaƙi da kuma ƙera bama-bamai a ƙasashen Mali da Libya.

Ta ce Mamuda ya samu horo na musamman daga malamai masu tsattsauran ra’ayi a tsakanin 2013 da 2015.

Hakazalika, suna da hannu a sace manyan mutane, ciki har da sace wani Injiniya ɗan ƙasar Faransa, Francis Collomp a 2013 da kuma sace Alhaji Musa Umar Uba, Magajin Garin Daura a 2019.

Ana kuma zarginsu da fashi da makami da kuma shirin kai hari wajen wani haƙar uranium a Nijar, wanda shirin nasu bai yi nasara ba.

Mai Bai wa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu ne, ya tabbatar da kama su yayin wani samamen haɗin gwiwa da jami’an tsaro suka kai.

Ribadu ya ce kama su zai kawo wa shugabancin ƙungiyar ta Ansaru koma baya.

Ansaru ta ɓalle daga cikin Boko Haram a 2012, inda da farko ta bayyana kanta a matsayin ƙungiya mai “tausaya wa al’umma.”

Amma daga baya ta haɗu da ƙungiyoyin ta’addanci na ƙasa da ƙasa, har ta ɗauki tambarin Al-Qaeda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ansaru Kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewa, wata gobara ta ƙone wani shagon Adidas Sports da ke cikin rukunin babban kantin nan na sayar da kayayyaki na Jabi Lake Mall, Abuja da tsakar daren Alhamis.

Daily Trust ta ruwaito cewa, shagon ne kaɗai gobarar ta shafa.

An kuma samu rahoton cewa, an baza jami’an kashe gobara daga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da na Kamfanin Berger da na hukumar kashe gobara ta Abuja da kuma jami’an ’yan sanda zuwa wurin.

Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29

A lokacin da Wakilin Daily Trust ya kai ziyara da safe zuwa wurin, an shawo kan gobarar.

Wani ma’aikaci a shagon ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na tsakar daren ranar Alhamis.

Ya ce, ba a samu asarar rai ba a wurin. Ya kuma tabbatar da cewa, “Shagon sayar da kayan Wasannin Adidas ne kawai gobarar ta shafa.”

Mai magana da yawun Hukumar kashe gobara ta babban birnin tarayya, Ibrahim Mohammad, ya tabbatarwa da majiyar da faruwar lamarin, amma ya ce ƙarama ce.

Ya ce, an shawo kan lamarin kuma an dawo da zaman lafiya.

Ita ma da take mayar da martani, kakakin rundunar ’yan sandan Birnin Tarayya, Josephine Adeh ta ce an tura jami’an ’yan sanda wurin da lamarin ya faru domin kare yankin da kuma hana sace-sacen jama’a.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:40 na asubahi, nan take muka tura mutanenmu wurin domin su tsare wurin da kuma hana duk wani abu da ya saɓa wa zaman lafiya,” in ji ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
  • Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba