Aminiya:
2025-11-02@19:43:50 GMT

Hilda Baci ta kafa tarihin dafa shinkafa buhu 200 a tukunya guda

Published: 13th, September 2025 GMT

Chef Hilda Baci mai shekara 28 ta kama hanyar kafa sabon tarihin girka shinkafa dafa-duka (Jollof) ’yar Najeriya mafi yawa a duniya.

Hilda Baci ta kafa wannan sabon tarihi ne inda ta girka shinkafa basmati buhu 200 a wata katafariyar tukunya a bainar jama’a.

Ta yi wannan sabon abin bajinta ce shekara biyu kacal bayan ta shiga kundin tarihi na duniya na Guinness a matsayin wadda ta shafe awanni mafiya yawa tana girke-girke a duniya.

A ranar Juma’a ta fara girkin a otel ɗin Eko Hotel & Suites, da ke Legas, kuma sama da mutum 20,000 mashahurai da sauransu sun yi rajista don halarta.

An kama buhun tabar wiwi 150 bayan hatsarin mota a Kano Abba ya tarbi tagwayen da aka raba da juna bayan yi musu tiyata a Saudiyya

Girman tukunyar da aka ƙera musamman domin wannan girki mai cike da tarihi ya kai murabba’in mita 6×6 (faɗi da tsawo), kuma taba iya ɗaukar lita 22,619.

Da farko Hilda ta shirya amfani da buhu 250 (kilogiram 5,000) na shinkafa samfurin basmati. Amma saboda matsalolin awon kayan, sai aka rage zuwa bubu 100 (kilogiram 4,000).

Kafin fara girkin a ranar Juma’a, Hilda Ta rubuta a shafinta na Inatagram cewa, wannan ƙoƙarin ba a fatar baka ba ne kawai, amma “tarihi ne a keɓaɓɓe,” ta ƙara da cewa duk wanda ya halarci taron zai ci abincin da aka girka kyauta.”

A bidiyo da aka gani kafin lokacin, an ga Hilda da mahaifiyarta suna addu’a a wajen gaban katafariyar tukunyar.

An kuma gan ta ta hau tukunyar don ta wanke ta da kanta. Ta ƙara da cewa, “E, zan iya tabbatar da cewa wannan tukunya tana da tsabfta sosai. Na naɗe hannuwana na wanke ta da kaina,” kamar yadda ya rubuta a Instagram.

Ta yi alƙawarin cewa abincin zai kasance “mafi kyau, mai tsafta da za ka taɓa ci a rayuwarka.”

Shirye-shiryen girkin

Tukunyar an ƙera ta musamman a yankin Kudu maso Yamma, kuma aikin ya ɗauki kusan wata uku.

Samun kayan ya ɗauki kusan wata biyu, haɗawa da gwaji kuwa wata ɗaya.

Shinkafar za ta ƙara yawa bayan ta nuna, zuwa kimanin kilogiram 14,000–16,000, kuma za ta wadatar da wa dubban mutane.

Hilda ta ce za ta yi amfani da ilimin lissafi da lura wajen daidaita kayan miya da kayan ƙamshi da sauran kayan haɗi a girkin. 

Kayan haɗi

Kayan haɗin girkin sun haɗa da kilogiram 1,000 na tumatir, albasa kilogram 600, kilogram 750 na man girki.

Sai kuma kayan ƙamshi irin su barkono (fresh cayenne pepper), paprika, thyme, basil, tafarnuwa, citta da sauran su.

An kuma sanya naman talotalo da sauransu don ƙarin ɗanɗano.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa

Madagascar ta sanar da kafa sabuwar gwamnati wadda ta kunshi fitattun ‘yan adawa guda uku a manyan mukamai na ministoci.

An gabatar da majalisar ministoci mai mambobi 29, wacce ta kunshi mata 10, a wani biki da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Yavoloha da ke babban birnin kasar, Antananarivo.

Shugaban rikon kwarya Michael Randrianireina ya bayyana a lokacin bikin cewa manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta sa gaba sun hada da yaki da rashin adalci, aiwatar da matakan tsuke bakin aljihu, da kuma samar da yanayin kasuwanci mai dorewa.

Ya kara da cewa kowane minista dole ne ya samar da sakamako mai kyau cikin watanni biyu, yana mai gargadin cewa rashin yin hakan a cikin wannan lokacin zai zama gazawa kuma zai iya haifar da maye gurbin minister a nan take.

An nada Christine Razanahasoa, tsohuwar Ministar Shari’a kuma tsohuwar Kakakin Majalisar Dokoki ta Kasa, a matsayin Ministar Harkokin Waje, kuma an nada Fanerisoua Irinavo, tsohuwar alkali wacce ta dawo daga gudun hijira daga  Faransa, a matsayin Ministar Shari’a.

An nada Hanitra Razavimanantsoa, ​​’yar majalisa daga jam’iyyar Tiaco Madagascar karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar Marc Ravalomanana, a matsayin Ministar Kasa a ma’aikatar Sake Gina Kasa. Waɗannan mutane uku suna wakiltar muryoyin  manyan bangarorin ‘yan adawa a Madagascar.

Jagoran juyin mulkin, Michel Randrianireina, ya kwace mulki a ranar 14 ga Oktoba bayan tsohon shugaban kasar Andry Rajoelina ya tsere daga kasar a cikin jirgin saman sojojin Faransa bayan makonni na zanga-zanga.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa