“Mutanen Zamfara ba wawaye ba ne. Gwamnan ya kamata ya daina waɗannan maganganun ƙarya, ya daina farfaganda, ya kuma haɗa kai da masu ruwa da tsaki na gaskiya don magance matsalar tsaro,” in ji Gummi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara

Hukumar Tsaro ta DSS ta kama wani likita da ake zargin yana ba da magunguna tare da kula da ’yan bindiga masu garkuwa da mutane da ke wasu sassan jihar Kwara.

An kama wanda ake zargin, wanda ba a iya gano sunansa ba a lokacin rahoton, a yankin Jebba bayan rahotannin sirri sun nuna cewa wasu masu safarar kaya suna kai magunguna daga Sakkwato domin kula da ’yan fashin daji da suka samu raunuka a dazukan jihar.

Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi

Majiyoyin tsaro sun ce da dama daga cikin waɗannan ƙungiyoyin masu laifi sun samu raunukan harbin bindiga a fafatawar da suka yi da jami’an tsaro a baya-bayan nan.

“Saboda haka muna ba da shawarar ƙara tsaurara matakan tsaro a cibiyoyin lafiya da ke cikin dazuka, domin masu garkuwa da mutane na iya kai hari a wuraren,” in ji wani jami’in tsaro.

Mai magana da yawun gwamnan jihar ta Kwara, Rafiu Ajakaye, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa kamun wata babbar nasara ce a ƙoƙarin da ake ci gaba da yi kan ’yan fashin daji.

“Wannan babban mataki ne daga DSS. Ya ƙara tabbatar da cewa hukumomin tsaro suna matsawa wa waɗannan ’yan ta’adda, suna kuma toshe hanyoyin tallafi da ke ba su damar gudanar da ayyukansu,” in ji shi.

Ajakaye ya ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa da hukumomin tsaro domin rufe dukkan hanyoyin da ke taimaka wa ayyukan garkuwa da mutane.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Nigeria: Har Yanzu Da Akwai Daliban Makaranta 250 Da Suke Hannun Masu Garkuwa Da Su
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara