HausaTv:
2025-09-17@20:28:14 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Qatar Zata Sauya Amurka A Matsayin Abokiyar Tsaron

Published: 13th, September 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhakan, sharbin bayan labarammu a yau zasu yi magana dangane da ‘yiyuwar gwamnatin kasar Qatar ta nemi maye gurbim Amurka a bangaren tsaron kasarta, bayan cin amanan da Amurka ta yi a ranar talatan da ta gabata.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday, ta nakalto wani shafin labarai na yanar gizo a Amurka ‘Axios’.

A ranar Alhamis da ta gabata ce, shafin yanar gizo na Acios na labarai ya nakalto Firay ministan kasar Qatar tana fadawa  fadar white House kan cewa, bayan saba alkawalin da Washington ta yi, dangane da hare-haren da HKI ta kaiwa birnin Doha, Qatar zata sake duba yarjeniyar tsaron da ke tsakaninta da Amurka ta kuma nemi sabon abokin aiki a wannan bangaren.

Axious ta kara da cewa, tunda Benyamin Natanyaho bai tuntubi Washington ko Trump ko kuma wani babban Jami’an gwamnatinsa kafin ya kai hare-haren da ya kai kan doha,!, al-amarin ya fi hatsari idan ya zo kan kasashen duniya, wadanda suka dogara da Amurka don tsaron kasashensu. Anan Amurka zata rasa aminci da yardar da take da shi take da shi  daga  wasu kasashenata.

Labarin ya kara da cewa Firay ministan kasar ta Qatar Muhammad bin Abdurrahman bin Jassim Al-thani, ya fadawa fadar whitehouse, bayan wannan yaudarar kasarsa zata nemi wani amintacce wanda zai maye gurbin Amurka.

Al-thani ya fadawa tashar talabijan ta CNN kan cewa a halin yanzu kasashen larabawa na yankin tekun farisa suna tattauna yadda zasu maida martani ga wannan al-amarin saboda wasu kasashen yankin da dama suna dogaro da Amurka don tabbatar da tsaron kasashensu. Don haka hare-hare kan Doha ya shafi dukkan wadan nan kasashe.

Har’ila yau rahoton ya bayyana cewa, bayan hare-haren da JMI ta kaiwa Al-udait ‘Air Base” a cikin yakin kwanaki 12 wanda Amurka ta jefa boma-bomai kan cibiyar makamashin nukliya na kasar, da kuma hare-haren da HKI kan Doha, Qatar tana ganin dole ta sake lalen harkokin tsaron kasar.

Rahoton ya ce, Al Thani ya fadawa Steve Witkoff, jakadan Amurka na musamman a gabas ta tsakiya kan cewa, Qatar zata sake duba harkokin tsaron kasar , musamman tare da Amurka saboda samun cikekken tsaro ga kasar.

Dangane da wannan shafin yanar gizo na labarai ‘Axios ta sami wani bayani da ke cewa shugaban Trump ya bukuci Natanyahu ya dauki alkali ba zai sake kaiwa kasar Qatar hare-hare ba.

Sannan bayan haka, Natanyahu bai nemi Afwar kasar Qatar ba, kuma ya ma yi alkawalin zai sake kai wasu hare-haren a kan doha idan bukatar haka ta kama.

 Qatar dai itace kasar Larabawa ta 7  wacce HKI ta yiwa ruwan boma bomai tun bayana fara yaki a gaza a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta, banda Gaza da yankin yamma da kogin Jordan, yahudawan sun kai hare-hare kan Lebanon, Syriya Iraki, Iran da kuma ita Qatar

Axios ya bayyana cewa a ranar Talatan da Natanyahu ya kai hare-hare kan Doha, shugaba Trump ya kira Natanyahu ta wayar tarho, har sau biyu, da farko yay a bayyana rashin aqmincewa da kai hare-haren, sannan tare da tambayarsa menene amfani na dogon zangon da HKI zata samu,

Wani tsohon jami’in gwamnatin Amurka ya bayyana cewa, Firay ministan kasar Qatar ya na daukar hare-haren a matsayin yaudara daga Tel’viv da kuma washingtong gaba daya.

Banda haka Benyamin Natanyahu ya fito a ranar Laraba yana fadar cewa yayi dai dai a hare-haren da ya kai Doha, sannan idan yan kungiyar Hamas sun ci gaba da kasancewa a kasar Qatar zai sake kai masu hare-hare.

Sannan ya kara da cewa hare-harensa a kan doha yana dai dai da hare-haren Amurka a kan Afganistan da Pakistan a lokacinda take neman  kungiyar Al-Qaeda bayan   ga watan Satumba.

Al-thani ya fadawa CNN kan cewa dole a hukunta Natanyahu, saboda keta hurumin kasa mai cikekken yanzi, wanda yin hakan ya sabawa dokokin kasa da kasa tare da kiranta Yar ta’adda.

Daga karshe Althani ya bayyana cewa, a halin yanzu tana tattaunawa da sauran kasashen larabawa na yankin tekun farisa, inda zasu iya maida martanin da zai sanya yankin shiga hatsari.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Adadin wadanda sukayi shahada sakamakon kisan kare dangi na Isra’ila ya kai 64,756 September 13, 2025 Unicef : Yara na cikin ukuba sanadin shingen Isra’ila a Gaza September 13, 2025 Araqchi: Babu Dalilin Jin Tsoron Tattaunawa September 12, 2025 Welayati: Abin Kunya Ne Yadda Duniya Ta Yi Shiru Kan Laifukan Isra’ila September 12, 2025 Ayatullah Khatami Ya Ja Hankalin Kasashen Larabawa Kan Hare-Haren Isra’ila September 12, 2025 Gaza: Falastinawa 48 Suka Yi Shahada A Hare-Haren Isra’ila September 12, 2025 Jagororin Hamas Sun Kubuta Daga Kisan Gillar Isra’ila Ne A Lokacin Da Suka Tafi Yin Sallah September 12, 2025 Qatar : shugabannin Isra’ila na kishirwar jefa duniya cikin rikici September 12, 2025 Guteress ya tattauna da Araghchi kan shirin shurin nukiliyar Iran  September 12, 2025 Netanyahu, ya sha alwashin dakile kafa kasar falasdinawa September 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ya bayyana cewa kai hare hare hare haren da a hare haren kasar Qatar

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar

Mamban a majalisar koli ta siyasar kasar Yemen ya aika sako ga mahalarta taron birnin Doha fadar mulkin kasar Qatar

Mohammed Ali al-Houthi, mamba a majalisar koli ta siyasar kasar Yemen, ya aike da sako ga shugabannin kasashen Larabawa da na kasashen musulmi da suka hallara a yau, Litinin, a taron Doha. Wannan taron na zuwa ne biyo bayan ha’incin yahudawan sahayoniyya da suka yi yunkurin halaka tawagar Hamas a babban birnin kasar Qatar.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, al-Houthi ya ce: “Sakonsa ga taron da za a yi a yau Litinin a birnin Doha na kasar Qatar, shi ne cewa: Matsayi mafi karfi shi ne tabbatar da halaccin jihadi da ‘yan mamaya da goyon bayan gwagwarmaya da kuma ayyana Isra’ila a matsayar ‘yar ta’adda.”

Ya kara da cewa: “Wannan zai kawo karshen rikici tare da dakatar da tashe-tashen hankula da wuce gona da iri.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar