NAFDAC ta kama jabun maganin maleriya na ₦1.2bn a Legas
Published: 12th, September 2025 GMT
Hukumar da ke Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) ta kama jabun magungunan zazzaɓin cizon sauro (maleriya) da darajarsu ta kai sama da Naira biliyan ₦1.2bn a Legas.
Hukumar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a a shafinta na sada zumunta X, inda ta ce jami’anta sun kai samame a wani ɗakin ajiyar kaya da ke yankin Ilasa-Oshodi, inda aka gano katan 277 na jabun magungunan maleriya nau’in Malamal Forte.
NAFDAC ta ƙara da cewa, “Ta kama katan 277 na jabun magungunan zazzaɓin cizon sauro na Malamal Forte waɗanda kuɗinsu ya kai sama da biliyan ₦1.2, a wani ɗakin ajiyar kaya da ke unguwar Ilasa-Oshodi a Jihar Legas”.
A cewar Hukumar NAFDAC, an ɓoye magungunan da ba a yi wa rijista ba ne a cikin kwalaye masu masu rubutun Diclofenac Potassium 50mg da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba daga kamfanin Shanɗi Tianyuan Pharmaceuticals Group da ke Ƙasar China. An ayyana magungunan a matsayin na bogi a don gujewa amfani da su.
Darakta-Janar ta Hukumar NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye ta bayyana wannan samamen a matsayin wani mataki na murƙushe su.
“Wannan kama jabun magungunan wani ɓangare ne na ci gaba da ƙoƙarin da NAFDAC ke yi a faɗin ƙasar don kare lafiyar jama’a da kuma tabbatar da magunguna masu inganci ne kawai ’yan Najeriya ke amfani da su,” in ji ta.
Ta yi bayanin cewa hukumar ta ƙara sanya ido a tashoshin jiragen ruwa da ma’ajiyar kayayyaki a faɗin ƙasar nan, tare da yin aiki tare da sauran jami’an tsaro domin daƙile ’yan fasa kwauri da ke cika kasuwar da kayayyaki masu haɗari.
Adeyeye ya jaddada cewa, gwamnati na goyon bayan ƙarfafa yaƙin da hukumar ke yi da jabun magunguna.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Darakta Janar ta NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta jaddada ƙudurin hukumar tare da cikakken goyon bayan fadar shugaban ƙasa da ma’aikatar lafiya ta tarayya, na kawar da jabun magunguna da marasa inganci daga Najeriya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jabun magungunan zazzaɓin cizon sauro
এছাড়াও পড়ুন:
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Yadda kasashen yammacin duniya suka ki sauke nauyin dake wuyansu, ya danne wa kasashe masu tasowa hakkinsu. Misali, a lokacin da ake samun bazuwar annobar COVID-19, dimbin kasashen yamma sun yi ajiyar alluran rigakafi a gida, inda suka hana fitar da su zuwa ketare, da musayar fasahohi masu nasaba da su. Sai dai a lokacin, hukumomi masu kula da harkokin kasa da kasa, kamar su Hukumar Lafiya ta Duniya, da Majalisar Dinkin Duniya dukkansu sun kasa tilasta musu sauya manufofinsu. Wannan tsarin kasa da kasa, idan mun bar shi haka ba tare da wani sauyi ba, to, wata rana za mu ga an koma tsarin zalunci na zamanin mulkin mallaka, wanda zai yi barazana ga hakkin rayuwa, da raya kai na al’ummar kasashe masu tasowa. Ta haka za mu san cewa gyara ya riga ya wajaba.
Saboda haka, shawarar inganta jagorancin duniya ta zama wani abun dake biyan bukatun dake akwai a duniyarmu. Wannan ya sa ta samun karbuwa a tsakanin kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka. Inda shahararren dan jarida a Najeriya Lawal Sale, ya rubuta a cikin wani sharhinsa cewa, “Wannan shawara za ta haifar da karin kwanciyar hankali, da tabbas a duniyarmu mai cike da tashin hankali, musamman ma a nahiyar Afirka.” Kana a nasa bangare, Paul Frimpong, wani shehun malami dan kasar Ghana, ya ce shawarar nan “tana tabbatar da cewa tsarin jagorancin duniya ba zai ci gaba da zama karkashin mallakar wasu kasashe masu karfi ba.” Kana dan jaridar kasar Lesotho, Silence Charumbira, ya ce shirin na baiwa kananan kasashe damar zama masu hakikanin ‘yancin kai.
Ta wannan shawara ta inganta jagorancin duniya, za mu iya kara fahimtar halayyar kasar ta Sin. Ko da yake wani yanayin da duniyarmu ke ciki shi ne dishewar tauraron kasashen yamma, amma duk da haka, kasar Sin ba ta neman yin koyi da kasashen yamma wajen yin babakere a duniya. Tana neman gyara, da inganta tsare-tsaren kula da harkokin duniya, ta yadda za ta tabbatar da moriyar dukkan kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, maimakon kafa wani sabon tsari da ya saba wa tsarin kasa da kasa na yanzu. Dalilin da ya sa haka shi ne babban burin kasar Sin ta fuskar diflomasiyya, shi ne kafa al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga bil’adama, da kokarin tabbatar da ci gaban harkokinsu na bai daya.
Yayin da karin kasashe ke nuna goyon bayansu ga shawarar kula da al’amuran duniya da kasar Sin ta gabatar, tabbas za mu shaida hadin gwiwar karin mutane a duniya don neman wanzar da adalci, abin da zai haifar da damar tabbatar da daidaito da adalci a duniyarmu. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp