NAFDAC ta kama jabun maganin maleriya na ₦1.2bn a Legas
Published: 12th, September 2025 GMT
Hukumar da ke Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) ta kama jabun magungunan zazzaɓin cizon sauro (maleriya) da darajarsu ta kai sama da Naira biliyan ₦1.2bn a Legas.
Hukumar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a a shafinta na sada zumunta X, inda ta ce jami’anta sun kai samame a wani ɗakin ajiyar kaya da ke yankin Ilasa-Oshodi, inda aka gano katan 277 na jabun magungunan maleriya nau’in Malamal Forte.
NAFDAC ta ƙara da cewa, “Ta kama katan 277 na jabun magungunan zazzaɓin cizon sauro na Malamal Forte waɗanda kuɗinsu ya kai sama da biliyan ₦1.2, a wani ɗakin ajiyar kaya da ke unguwar Ilasa-Oshodi a Jihar Legas”.
A cewar Hukumar NAFDAC, an ɓoye magungunan da ba a yi wa rijista ba ne a cikin kwalaye masu masu rubutun Diclofenac Potassium 50mg da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba daga kamfanin Shanɗi Tianyuan Pharmaceuticals Group da ke Ƙasar China. An ayyana magungunan a matsayin na bogi a don gujewa amfani da su.
Darakta-Janar ta Hukumar NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye ta bayyana wannan samamen a matsayin wani mataki na murƙushe su.
“Wannan kama jabun magungunan wani ɓangare ne na ci gaba da ƙoƙarin da NAFDAC ke yi a faɗin ƙasar don kare lafiyar jama’a da kuma tabbatar da magunguna masu inganci ne kawai ’yan Najeriya ke amfani da su,” in ji ta.
Ta yi bayanin cewa hukumar ta ƙara sanya ido a tashoshin jiragen ruwa da ma’ajiyar kayayyaki a faɗin ƙasar nan, tare da yin aiki tare da sauran jami’an tsaro domin daƙile ’yan fasa kwauri da ke cika kasuwar da kayayyaki masu haɗari.
Adeyeye ya jaddada cewa, gwamnati na goyon bayan ƙarfafa yaƙin da hukumar ke yi da jabun magunguna.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Darakta Janar ta NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta jaddada ƙudurin hukumar tare da cikakken goyon bayan fadar shugaban ƙasa da ma’aikatar lafiya ta tarayya, na kawar da jabun magunguna da marasa inganci daga Najeriya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jabun magungunan zazzaɓin cizon sauro
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.