An kama buhun tabar wiwi 150 bayan hatsarin mota a Kano
Published: 13th, September 2025 GMT
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) ta kama buhu 150 maƙare da tabar wiwi a yayin da ake tsaka aikin ceto bayan wani hastarin mota da ya auku a kan babbar hanyar Zariya zuwa Kano.
Hukumar ta bayyana cewa hatsarin ya auku ne tsakanin wata mota ƙirar Volkswagen Golf da wata babbar mota a yankin Gadar Tamburawa da ke Jihar Kano.
Kakakin NDLEA na Jihar Kano, ASN Sadiq Mohammed Maigatari, ya bayyana cewa ɗaya daga cikin fasinjojin da aka ceto ya yi ƙoƙarin tserewa amma an yi nasarar kama shi.
Ya ce a yayin bincike ne aka gano buhuna 150 na tabar wiwin wanda nauyinsu ya kai kilogram 112.
Abba ya tarbi tagwayen da aka raba da juna bayan yi musu tiyata a SaudiyyaYa ƙara da cewa direban motar ya shaida musu cewa shi ne ya yiwo dakon tabar wiwin madadin mai ita, kuma ba wannan ne karon farko ba da ya yi safarar ta zuwa Kano da wasu wurare.
Direban ya bayyana cewa ya yi aron hannu ne domin kauce wa shingen binciken jami’an NDLEA, a garin haka aka samu hatsarin na ranar Asabar.
Ya ƙara da cewa direban babbar motar ya samu karaya, sauran mutum biyu da aka kama suke tsare.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gadar Tamburawa Hatsari hatsarin mota Tabar wiwi
এছাড়াও পড়ুন:
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana
Ƙwallon ɗaya tilo da kyaftin din ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars Ahmed Musa ya ciwa ƙungiyar tayi sanadiyar samun nasarar farko da ƙungiyar tayi tun bayan fara wannan kakar wasannin ta bana.
Pillars ta doke abokiyar karawarta Enugu Rangers da ci 1-0 a wasan da suka buga a filin wasa na Sani Abacha dake birnin Kano inda ɗaruruwan magoya bayan ƙungiyoyin biyu suka shaidi wasan.
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed MusaKafin yanzu ƙungiyar, mallakar gwamnatin jihar Kano ta yi rashin nasara biyu sannan ta buga canjaras ɗaya a wasanni uku da ta buga a wannan kakar, wannan nasarar da Sai Masu Gida suka samu ta sa ta koma matsayi na 17 a teburin gasar ta NPFL.
Pillars ta fara wasan na wannan mako da zimmar samun nasara bayan rashin nasarar da ta yi a hannun Katsina United a wasan Mako na 3 da suka buga a filin wasa na Muhammadu Dikko dake birnin Katsina, kyaftin Ahmed Musa wanda ya dawo daga raunin da yayi fama da shi, ya fitar wa Pillars kitse daga wuta a wasan na yau.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp