Wike ya goyi bayan Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a wani mataki da ya samu matsayin ministan Babban Birnin Tarayya Abuja.

Duk da yake har yanzu shi mamba ne na PDP, Wike ya kasance yana bayyana cewa zai ci gaba da kasancewa cikin jam’iyyar yayin da yake kuma yin aiki don sake zaɓen Tinubu, wani matsayin da yawancin mambobin PDP ba sa jin daɗinsa.

Kafin yanzu, jam’iyyar ta shiga cikin wata babbar matsala kan matsayin sakatare jam’iyyar na ƙasa, tsakanin Samuel Anyanwu, wanda Wike yake goyo baya, da Sunday Ude-Okoye, wanda yake samun goyon bayan Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah.

Mafi yawancin shugabannin jam’iyyar sun yi tunanin cewa idan har Anyanwu ya dawo a matsayin sakataren jam’iyyar na ƙasa zai kwantar da hankalin Wike. Amma kafin babban taron na Ibadan, ministan Abuja ya fito da sabbin sharuɗɗa.

Vangaren magoya bayan Wike sun gudanar da taro tare da shimfiɗa sabbin sharuɗɗa ta yadda za a iya gudanar da taron cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Cikin waɗanda suka halarci taron sun haɗa da tsofaffin gwamnonin, Samuel Ortom (Benuwai), Ifeanyi Ugwuanyi (Inugu), Ayo Fayose (Ekiti) da Okezie Ikpeazu (Abiya), da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Anyanwu.

Vangaren ya kafa sharaɗin cewa dole ne shugaban jam’iyyar na ƙasa ya fito daga yankin arewa na tsakiya bisa ga tsarin rabon muƙamai na yankuna na taron 2021.

A cewar ɓangaren, rashin bin ƙa’idojin da aka ambata zai sa tsarin babban taron ya ruguze ya zama mara inganci, saboda za a samu rarrabuwan kawuna a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

Sauran sharuɗɗan sun haɗa da yin kiran gaggawa ga kwamitin gudanarwa na ƙasa don gudanar da sabbin zaɓen shugabanni a jihohin Ebonyi da Anambra bisa ga hukuncin kotu da gudanar da sabon taron jam’iyyar na yankin kudu maso gabas da tabbatar da sakamakon taron kudu maso kudu da aka gudanar a Kalabar na Jihar Kuros Ribas, wanda kotu ta riga ta tabbatar da shi da kuma gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi na Jihar Ekiti cikin gaggawa bisa ga hukuncin kotu.

Amma yayin da yake magana a wajen ƙaddamar da kwamitin shirya taron mai mambobi 119 a hedkwatar PDP a Abuja, shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP, Bala Mohammed ya bayyana cewa ba za su ci gaba da yin shiru ba suna barin wasu mutane suna lalata musu jam’iyyar.

Ya yaba da jagorancin Damagum da ingancin kwamitin taron, yana cewa, “Babu shakku kan ƙarfin wannan shugabancin. Sun yi hakan a baya, kuma muna ganin za su yi iya bakin ƙoƙarinsu. Gwamnonin PDP suna tare da sauran ‘ya’yan jam’iyyar nan wajen jagoran wannan kwamitin.

Da yake jawabi kan wannan dambarwar, masanin harkokin siyasa, Farfesa Kamilu Sani Fage ya gargaɗi cewa PDP na fuskantar wata matsala idan ba ta ɗauki matakan gaggawa wajen magance buƙatun Wike ba.

Ya ce Wike ya zama ƙarfan ƙafa a cikin jam’iyyar, domin yana iya bayar da umurni bisa irin gina mabiyansa, inda ya ce waɗannan sabbin sharuɗɗan da ya gindaya sun saɓa da tsarin dimokuraɗiyya.

Fage ya ƙara da cewa Wike yana ta yaƙar PDP tun daga 2023 ta hanyar tallata Tinubu, karɓar muƙamin minista a gwamnatin APC, da kuma raunana PDP a ƙasa da kuma a Jihar Ribas.

Ya gargaɗi cewa “Jam’iyyar tana buƙatar tabbatar da ladaftarwa. Babu wanda ya mallaki PDP. Idan suka bar Wike ya ci gaba, zai haifar da babbar matsala.”

A cewarsa, PDP na fuskantar haɗarin maimaita taron 2015, idan ba ta ɗauki mataki ba. “Idan tana son ta tsaya da ƙafarta, dole ne ta ɗauki matsaya mai ƙarfi. In ba haka ba, abin da ya faru a 2015 na iya maimaituwa a 2027.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jam iyyar na ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

Da safiyar yau 17 ga watan Satumba, aka bude dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan karo na 12 da zai dauki kwanaki 3, daga raneku 17 zuwa 19 ga wannan nan, bisa jigon “daukaka tsarin duniya da inganta neman ci gaba cikin lumana”, a nan birnin Beijing.

Tawagogi sama da 100 na gwamnatocin kasashe daban-daban da yankuna da wakilan kungiyoyin kasa da kasa ne ke halartar taron, inda yawan masu rajista ya wuce 1,800.

Da safiyar yau, taron ya shirya tarukan tattaunawa guda 6 bisa jigon “ma’anar cimma nasarar yakin duniya na kin tafarkin murdiyya” da “madaidaitan hanyoyi da manyan kasashe za su bi na yin mu’ammala”, da “hanyoyin warware rikice-rikicen shiyya-shiyya”, da “cika shekaru 80 da kafuwar MDD: samun ci gaba cikin sauye-sauye”, da “amfani da sarrafa sabbin fasahohi”, da kuma “kirkire-kirkire a bangaren kimiyya da fasaha da sauye-sauyen yanayin yaki”. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
  • Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya