Aminiya:
2025-11-02@15:25:04 GMT

Daruruwan magoya bayan NNPP sun tarbi Kwankwaso a Kalaba

Published: 11th, September 2025 GMT

Daruruwan magoya bayan jam’iyyar NNPP ne suka taru a birnin Kalaba na Jihar Kuros Riba, domin tarbar jagoran jam’iyyar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, a wata ziyarar sada zumunta da ya kai a jihar.

Kwankwaso ya fara irin wannan ziyarar ce daga yankin Kudu maso Gabas, kafin ya wuce zuwa Kudu maso Kudu, inda ya sauka a Kalaba domin ganawa da mambobin jam’iyyar.

Kotu ta yanke wa jagoran Ansaru hukuncin ɗaurin shekaru 15 Trump ya tiso ƙeyar rukunin farko na ’yan Najeriya daga Amurka

A yayin da yake jawabi ga taron magoya bayan jam’iyyar a Kalaba, tsohon Gwamnan Kano, ya bayyana cewa wannan ziyara ba ta da alaƙa da yaƙin neman zaɓe.

Sai dai ya ce uzuri ne ya kai shi yankin Kudu maso Gabas, kuma ya yanke shawarar tsayawa a Kalaba domin gaisawa da magoya bayan jam’iyya.

“Ziyarar da na kawo muku ba yaƙin neman zabe ba ne, domin lokacin kamfe bai yi ba. Na zo ne saboda wani uzuri da ya kawo ni wannan yanki, amma na ce sai na tsaya na ganku, mu gaisa, mu sada zumunci.”

Ya ja hankalin mambobin jam’iyyar da su zauna lafiya da jama’ar yankin da suke zaune da su, yana mai cewa: “A rayuwa dole mu riƙa zama lafiya da mutanen yankin da muke ciki.”

Kwankwaso ya kuma shawarci mambobin jam’iyyar da su tabbatar sun yi rajista ko sabunta katin zabe, domin kasancewa cikin shiri idan lokacin zabe ya yi.

A nasa jawabin, shugaban matasan jam’iyyar NNPP a Jihar Kuros Riba, Alhaji Muhammad Zanjuma, ya bayyana cewa jam’iyyar na da ɗimbin magoya baya a jihar.

“Wasu ma ba su san da zuwan jagoran ba, amma da ka ga yadda jama’a za su cika wurin nan, za ka san jam’iyyar na da ƙarfi. Idan aka kada gangar siyasa yau, lallai NNPP za ta taka muhimmiyar rawa,” in ji shi.

Shi ma a nasa bangare, jami’in hulda da jama’a na jam’iyyar a jihar, kuma wakilin ‘yan Arewa, Umar Darki  wanda aka fi sani da Umar Police, ya ce wannan ziyara da Kwankwaso ya kawo ta ƙara jaddada cewa bai manta da ’yan Arewa mazauna Kudancin Najeriya ba.

“Muna godiya da irin kulawar da yake yi mana, musamman idan wani abu ya faru da ’yan Arewa a Kudu, yana shiga cikin lamarin. Allah Ya saka masa da alheri,” in ji Umar Police.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rabiu Musu Kwankwaso magoya bayan

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan

Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta nuna damuwarta game da irin tashin hankali da ake ciki a Sudan musamman a yankin El Fasher.    

Iran ta sake jaddada goyon bayanta ga ‘yancin Sudan, da hadin kai, da kuma cikakken yankin kasar yayin da tashin hankali ya mamaye kasar dake Arewacin Afirka.  

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta waray tarho da takwaransa na Sudan Mohiuddin Salem a ranar Juma’a.

Na farko ya nuna damuwa musamman game da hare-hare da kisan gillar da aka yi wa fararen hula a birnin El Fasher da ke kudu maso yammacin Sudan.

Duniya ta damu matuka a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar tashin hankali a Sudan.

A ranar Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya bayyana matukar damuwa game da rikice-rikicen makamai da ake ci gaba da yi a El Fasher, yana mai Allah wadai da lalata kayayyakin more rayuwa da kuma kisan fararen hula a birnin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan