Sanarwar ta ƙara da cewa, SABER wani shiri ne na shekaru biyar, wanda ya dogara da aiki, wanda Bankin Funiya ke tallafawa, wanda aka tsara shi cikin tsanaki domin wargaza shingayen faɗuwar jari, da zaburar da sana’o’i masu zaman kansu, da samar da ayyukan yi masu ɗorewa ga al’ummar Zamfara.

 

Za a raba Naira 150,000 ga mutum 2,000 a faɗin jihar domin tallafa wa ƙananan sana’o’i.

Bugu da ƙari, mutane 1,000 a ƙanana da matsakaitan sana’o’i za su karbi Naira 500,000 kowanne. Haka kuma, mutane 60 daga matsakaita da manyan ‘yan kasuwa za su ci gajiyar tallafin Naira miliyan biyar kowannen su.

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, SABER ba wani abu ba ne na yau da kullum, inda ya tabbatar da cewa adadin kuɗaɗen da aka ware domin gudanar da ayyukan shirin ya kai kusan Naira Biliyan 1.1, tare da tallafin da ya kai dalar Amurka miliyan 20 zuwa dala miliyan 52 tsakanin shekarar 2022 zuwa 2026.

 

“Mun taru ne a yau domin ƙaddamar da shirin tare da fara bayar da kuɗaɗe don tallafa wa ‘yan kasuwa da mata daban-daban a fafin jihar nan.

 

“Akwai manyan nau’o’i uku na kuɗaɗen da za a biya, mun yi nazari sosai kan cibiyoyin gwamnati da kuma kamfanoni masu zaman kansu, waɗanda shugabannin ƙungiyar ‘yan kasuwa ke wakilta, don zabar waɗanda za su ci gajiyar kowane fanni na tallafin.

 

Gwamna Lawal ya ci gaba da jaddada cewa shirin na SABER wanda ma’aikatar kasafin kuɗi da tsare-tsare ta shirya shi, ma’aikatu daban-daban ne ke aiwatar da shi, waɗanda suka haɗa da ma’aikatar kasuwanci da masana’antu, ZAGIS, da sauran su kamar kuɗi, noma, da shari’a. Hakanan ya ƙunshi ayyuka na Harajin Cikin Gida, Kamfanin Gidaje, da ZITDA, suna aiki tare don samar da sauƙin kasuwanci.

 

Tun da farko, Babban Darakta na Hukumar Raya Ƙanana da Matsakaitan Masana’antu ta Nijeriya (SMEDAN), Charles Odii, ya yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa ɗimbin ƙoƙarinsa na tallafa wa ‘yan kasuwa na cikin gida a Jihar Zamfara.

 

“Na ji daɗin yadda gwamna ke bakin ƙoƙarinsa wajen bunƙasa ƙananan sana’o’i a Nijeriya, ina zaune na ji cewa ‘yan kasuwa 2,000 za su samu Naira 150,000. Ina ganin yana da muhimmanci idan ƙaramin ɗan kasuwa ya samu Naira 150,000, zai ɗauki mutum ɗaya aiki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.

A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Ya bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.

Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.

Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.

TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.

Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”

Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.

Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.

Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar