Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Published: 12th, September 2025 GMT
Sanarwar ta ƙara da cewa, SABER wani shiri ne na shekaru biyar, wanda ya dogara da aiki, wanda Bankin Funiya ke tallafawa, wanda aka tsara shi cikin tsanaki domin wargaza shingayen faɗuwar jari, da zaburar da sana’o’i masu zaman kansu, da samar da ayyukan yi masu ɗorewa ga al’ummar Zamfara.
Za a raba Naira 150,000 ga mutum 2,000 a faɗin jihar domin tallafa wa ƙananan sana’o’i.
A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, SABER ba wani abu ba ne na yau da kullum, inda ya tabbatar da cewa adadin kuɗaɗen da aka ware domin gudanar da ayyukan shirin ya kai kusan Naira Biliyan 1.1, tare da tallafin da ya kai dalar Amurka miliyan 20 zuwa dala miliyan 52 tsakanin shekarar 2022 zuwa 2026.
“Mun taru ne a yau domin ƙaddamar da shirin tare da fara bayar da kuɗaɗe don tallafa wa ‘yan kasuwa da mata daban-daban a fafin jihar nan.
“Akwai manyan nau’o’i uku na kuɗaɗen da za a biya, mun yi nazari sosai kan cibiyoyin gwamnati da kuma kamfanoni masu zaman kansu, waɗanda shugabannin ƙungiyar ‘yan kasuwa ke wakilta, don zabar waɗanda za su ci gajiyar kowane fanni na tallafin.
Gwamna Lawal ya ci gaba da jaddada cewa shirin na SABER wanda ma’aikatar kasafin kuɗi da tsare-tsare ta shirya shi, ma’aikatu daban-daban ne ke aiwatar da shi, waɗanda suka haɗa da ma’aikatar kasuwanci da masana’antu, ZAGIS, da sauran su kamar kuɗi, noma, da shari’a. Hakanan ya ƙunshi ayyuka na Harajin Cikin Gida, Kamfanin Gidaje, da ZITDA, suna aiki tare don samar da sauƙin kasuwanci.
Tun da farko, Babban Darakta na Hukumar Raya Ƙanana da Matsakaitan Masana’antu ta Nijeriya (SMEDAN), Charles Odii, ya yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa ɗimbin ƙoƙarinsa na tallafa wa ‘yan kasuwa na cikin gida a Jihar Zamfara.
“Na ji daɗin yadda gwamna ke bakin ƙoƙarinsa wajen bunƙasa ƙananan sana’o’i a Nijeriya, ina zaune na ji cewa ‘yan kasuwa 2,000 za su samu Naira 150,000. Ina ganin yana da muhimmanci idan ƙaramin ɗan kasuwa ya samu Naira 150,000, zai ɗauki mutum ɗaya aiki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
A wani bidiyo daban da PUNCH Metro ta gani a Facebook, wanda Mc Pee ya wallafa, wani mutum da ake zargin dalibi ne na jami’ar ya bayyana abin da ya faru.
A cewarsa, marigayin ya roki a bar shi ya rayu kafin daga bisani wanda ake zargin ya kashe shi.
Ya ce: “Nanpon ya riga ya yanke Peter a kumatunsa yayin da yake rokon a bar shi. Lokacin da muka shiga tsakani muka ce ya daina, sai ya yi barazanar yanka duk wanda ya kusanto shi.
“Da Peter ya ga ba ya sauraron rokonsa, sai ya rungume shi yana rokonsa da kuka.
“Mun fita neman taimako amma babu wanda ya amsa mana. Da Peter ya yi kokarin tserewa sai ya fadi, Nanpon ya kamo shi ya ci gaba da saransa da adda.”
Wani kwararren masanin tsaro da yaki da ta’addanci ya wallafa a dandalin D a ranar Lahadi cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Jihar Filato sun kama wanda ake zargin.
Ya kuma ambaci majiyoyi da suka tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaro na jami’ar.
Ya rubuta cewa, “Rundunar ‘Yansanda ta Filato ta kama wani dalibi mai shekaru 23 na Jami’ar Jos bisa zargin kashe abokinsa sannan ya binne shi a rami mara zurfi a cikin dakinsa da ke kauyen Rusau a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.
“Majiyoyi sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi a Jos, inda suka danganta da rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaron jami’ar.
“A cewar majiyoyin, wanda ake zargin mai suna Dabid Nanpon Timmap, dalibi a matakin shekara ta uku a jami’ar, ya kai wa Peter Mata Mafurai, mai shekaru 22, hari da adda, ya kashe shi a gidansa.”
Zagazola ya kara da cewa, bayan samun kiran gaggawa da misalin karfe 9:30 na safiya, DPO na sashin Laranto ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa wurin, inda aka kama wanda ake zargin.
“Majiyoyin sun ce bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya binne mamacin a cikin rami mara zurfi da ya haka a cikin dakinsa. An tono gawar kuma an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham domin yin binciken gawar (autopsy),” in ji shi.
Ya kara da cewa, an tsare wanda ake zargin yayin da ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin dalilin kashe abokin nasa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA