Aminiya:
2025-11-02@12:37:54 GMT

Abba ya tarbi tagwayen da aka raba da juna bayan yi musu tiyata a Saudiyya

Published: 13th, September 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya tarbi tagwayen da aka haifa manne da juna, inda aka raba su da juna ta hanyar yi musu tiyata a Ƙasar Saudiyya.

Tagwayen waɗanda ’yan asalin Najeriya ne, sun iso filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, inda tawagar Saudiyya ta tarbe su.

Ambaliya: SEMA ta raba kayan tallafi ga gidaje 90 a Gombe ’Yan bindiga sun harbi fasinjoji 2, sun sace makiyaya a Neja

An yi musu tiyata a Asibitin Ƙwararru na Yara King Abdullah da ke Riyadh, bisa umarnin Sarki Salman bin Abdulaziz Al-Saud da Yarima Mohammed bin Salman.

Hassana da Husaina sun tafi Saudiyya tun a watan Oktoban 2023, inda likitoci suka gano cewa suna manne da juna ne ta ƙasan cikinsu, ƙugu da ƙashin baya, lamarin da ya sa matsalar ta yi tsanani.

Tawagar ƙwararrun likitoci 38 daga fannoni daban-daban kamar masu tiyatar yara, k5wakwalwa, ƙashi, fitsari da fata ne, suka shafe sa’o’i 14 suna aiki a matakai tara kafin su raba su cikin nasara.

Wannan aiki ya kasance ɗaya daga cikin mafi wahala amma ya yi nasara cikin shirin Saudiyya na raba tagwaye.

Jakadan Saudiyya a Kano, Khalil Ahmed Al-Admawi, ya yaba da nasarar aikin, inda ya bayyana cewa hakan alama ce ta jajircewar Saudiyya wajen taimakon bil adama.

Ya kuma ce za su ci gaba da tallafa wa ƙasashe irin su Najeriya ta hanyar Cibiyar Agaji ta Sarki Salman.

A nasa jawabin, Gwamna Abba ya yi alƙawarin ɗaukar nauyin kula da lafiyar tagwayen, iliminsu da sauran buƙatunsu na yau da kullum.

Wannan ita ce tiyatar raba tagwaye ta 65 da aka yi nasara a shirin Saudiyya, wadda ta taimaka wa tagwaye 150 daga ƙasashe 25 cikin shekaru 35 da suka wuce.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cibiya Gwamna Abba Nasara Rabawa Saudiyya Tagwaye Tiyata

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Wannan mataki ne awanni kaɗan bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da Anyanwu da wasu mutane uku, lamarin da ya ƙara ta’azzaea rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo