Ambaliya: SEMA ta raba kayan tallafi ga gidaje 90 a Gombe
Published: 13th, September 2025 GMT
Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Gombe (SEMA) ta raba kayan tallafi ga al’ummar Jalingo-Kamo da ambaliyar ruwa ta shafa a Karamar Hukumar Kaltungo, inda iftila”in ya shafi gidaje kimanin 90.
Rabon kayan ya biyo bayan umarnin Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, wanda ya amince da bayar da kayan abinci da na masarufi domin rage raɗaɗin da jama’ar da abin ya shafa suke ciki.
Yayin rabon kayan a fadar Hakimin Jalingo-Kamo, Sakataren Hukumar SEMA, Alhaji Abdullahi Haruna Abdullahi ya ce sun gudanar da cikakken bincike da ƙirga waɗanda abin ya shafa kafin rabon.
Abdullahi ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici tare da isar da saƙon ta’aziyyar Gwamnan ga al’ummar da iftila’in ta rutsa da su.
Ya jaddada cewa, tallafin an bayar da shi ne don rage wahala ba wai a matsayin diyya ba.
A nasa jawabin, Jagoran Majalisar Dokokin Jihar Gombe kuma Ɗan Majalisa mai wakiltar Kaltungo ta Gabas, Yerima Ladan Gaule ya yi ta’aziyya ga waɗanda abin ya shafa tare da tabbatar musu da ƙudirin gwamnati na ci gaba da kula da al’umma a kowanne hali.
Ya kuma buƙaci jama’a su ci gaba da mara wa gwamnatin Inuwa Yahaya baya domin ci gaban jihar.
Da yake mayar da jawabi Hakimin Jalingo-Kamo, Alhaji Abdullahi Musa a madadin waɗanda iftila’in ya shafa ya gode wa Gwamna Inuwa Yahaya, da Ɗan majalisar da Hukumar SEMA bisa wannan taimako.
Sai dai ya roƙi gwamnati da ta gina hanyoyin mota domin bunƙasa ci gaban yankin tare da samar da fitilun titi don inganta tsaro.
Kayan da aka raba sun haɗa da: Buhunan shinkafa da taliya da tabarma da zannuwa da tufafin yara da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Inuwa Yahaya
এছাড়াও পড়ুন:
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar SDP a zaben 2023, Adewole Adebayo, ya ce Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ba shi da burin da ya wuce na tara haraji tun yana Gwamna a Legas.
Adebayo ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels.
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaA cewarsa, “Kowa ya san cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu sananne ne wajen karbar haraji. Amma wannan tsarin karbar haraji ya fi tsarin da ya tarar da shi wanda ba shi da tsari.
“Ya yi hakan a Legas, sannan ya zo Abuja domin ya dora daga inda ya tsaya a Legas.”
Sai dai Adebayo ya ce Tinubu ya yi kokari wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya.
“A bayyane yake cewa tattalin arzikin da Shugaba Buhari ya bari ba a tafiyar da shi yadda ya kamata ba, kuma yana cikin mawuyacin yanayi kamar na mara lafiya da aka kai dakin jinya. Kamar yadda likita ke bukatar yin cikakken bincike domin gano matsalar mara lafiyan, haka ma ake bukatar fahimtar matsalar tattalin arziki kafin a fara warkar da ita.
“Abin da Shugaba Tinubu ya yi shi ne ya daidaita marar lafiyan, amma ban tabbatar ko ya kai ga gano matsalar ba. Don haka mara lafiyar ba zai mutu nan da nan ba, amma kuma ba a samo maganin cutar shi ba.
“Ba a gano ciwon da ke damun mara lafiyan ba, amma a matsayinsa na likita, yana daukar wasu matakai. Wasu daga cikin matakan ma sun kara ciwon mara lafiyar, amma sannu a hankali likitan yana samun nasara a wasu bangarorin, wanda hakan ke sa wasu su yi tunanin cewa mara lafiyan na kan hanyar warkewa,” in ji Adebayo.