Aminiya:
2025-11-02@17:01:42 GMT

Ambaliya: SEMA ta raba kayan tallafi ga gidaje 90 a Gombe

Published: 13th, September 2025 GMT

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Gombe (SEMA) ta raba kayan tallafi ga al’ummar Jalingo-Kamo da ambaliyar ruwa ta shafa a Karamar Hukumar Kaltungo, inda iftila”in ya shafi gidaje kimanin 90.

Rabon kayan ya biyo bayan umarnin Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, wanda ya amince da bayar da kayan abinci da na masarufi domin rage raɗaɗin da jama’ar da abin ya shafa suke ciki.

NAFDAC ta kama jabun maganin maleriya na ₦1.2bn a Legas Harkar tsaro a gabashin Sakkwato na ƙara taɓarɓarewa — Sanata Lamiɗo

Yayin rabon kayan a fadar Hakimin Jalingo-Kamo, Sakataren Hukumar SEMA, Alhaji Abdullahi Haruna Abdullahi ya ce sun gudanar da cikakken bincike da ƙirga waɗanda abin ya shafa kafin rabon.

Abdullahi ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici tare da isar da saƙon ta’aziyyar Gwamnan ga al’ummar da iftila’in ta rutsa da su.

Ya jaddada cewa, tallafin an bayar da shi ne don rage wahala ba wai a matsayin diyya ba.

A nasa jawabin, Jagoran Majalisar Dokokin Jihar Gombe kuma Ɗan Majalisa mai wakiltar Kaltungo ta Gabas, Yerima Ladan Gaule ya yi ta’aziyya ga waɗanda abin ya shafa tare da tabbatar musu da ƙudirin gwamnati na ci gaba da kula da al’umma a kowanne hali.

 Ya kuma buƙaci jama’a su ci gaba da mara wa gwamnatin Inuwa Yahaya baya domin ci gaban jihar.

Da yake mayar da jawabi Hakimin Jalingo-Kamo, Alhaji Abdullahi Musa a madadin waɗanda iftila’in ya shafa  ya gode wa Gwamna Inuwa Yahaya, da Ɗan majalisar da Hukumar SEMA bisa wannan taimako.

Sai dai ya roƙi gwamnati da ta gina hanyoyin mota domin bunƙasa ci gaban yankin tare da samar da fitilun titi don inganta tsaro.

Kayan da aka raba sun haɗa da: Buhunan shinkafa da taliya da tabarma da zannuwa da tufafin yara da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Inuwa Yahaya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026

Gwamnatin Jihar Gombe ta ƙaddamar da taron sauraron ra’ayoyi jama’a kan shirye-shiryen tsara kasafin kuɗin shekarar 2026 a wani yunƙuri na jaddada ƙudirinta na gudanar da mulki cikin gaskiya da haɗin kai.

Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Gwamnan Jihar, Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna jajircewar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya wajen tabbatar da cewa ra’ayoyin jama’a na taka muhimmiyar rawa a tsara kasafin kuɗi da aiwatar da shi.

Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Ya ce tattaunawar ta bai wa gwamnati damar haɗa kai da sarakunan gargajiya, mata, matasa, ƙungiyoyin farar hula da sauran masu ruwa da tsaki, domin bayar da shawarwari kan muhimman fannoni kamar ilimi, lafiya, noma da gine-gine, da za su amfanar da al’umma baki ɗaya.

Dakta Jatau ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta samu ci gaba wajen alkinta kuɗaɗe cikin tsari da gaskiya, wanda hakan ya sa Gombe ke samun matsayi mai kyau a ɓangaren ingantaccen gudanar da kuɗi da sauƙin kasuwanci a Najeriya.

“Kasafin kuɗin 2026 zai mai da hankali ne kan ci gaba da ayyukan da ake yi, tare da ƙara zuba jari a muhimman fannoni, da tabbatar da daidaito da manufofin ci gaban ƙasa da na duniya,” in ji shi.

A nasa ɓangaren, Kwamishinan Kasafi da Tsare-Tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Salihu Baba Alkali, ya bayyana taron a matsayin wata hanya ta buɗe ƙofa tsakanin gwamnati da jama’a domin samun fahimta da amincewa.

Ya buƙaci mahalarta taron da su bayar da shawarwari masu amfani da za su taimaka wajen samar da kasafin kuɗin da zai kasance mai ɗorewa kuma mai amfani ga kowa da kowa.

Kwamishinan ya kuma gode wa mahalartan bisa yadda suka bayar da gudunmawa, yana mai tabbatar da cewa za a yi la’akari da shawarwarinsu a cikin tsarin ƙarshe na kasafin kuɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026