Aminiya:
2025-11-02@12:37:54 GMT

Matuƙin jirgin Air Peace na shan miyagun ƙwayoyi — Rahoton

Published: 12th, September 2025 GMT

Hukumar Binciken Hatsari ta Najeriya (NSIB) ta fitar da rahotonta na farko, inda ta tuhumi wani matuƙin jirgin sama na Air Peace da kuma wani ma’aikacin jirgin da laifin shan miyagun ƙwayoyi da barasa.

Masu binciken hatsarin sun gwada ma’aikatan jirgin cewa suna amfani da abubuwan da ake zargin su bayan da jirgin su da ya yi yunƙurin sauka tare da kauce hanya ba tare da izinin hakan ba a titin jirgin sama na filin jirgin sama na Fatakwal a ranar 13 ga Yuli, 2025.

’Yan Najeriya sun kusa fara shan wutar sa’o’i 24 babu ɗaukewa — Minista Likitoci sun tsunduma yajin aiki a fadin Najeriya

Hakan na ƙunshe ne a cikin wani rahoto na share fage mai ɗauke da sa hannun daraktan hulɗa da jama’a da taimakon iyali a hukumar NSIB, Madam Bimbo Olawumi Oladeji, wadda ta bayyanawa Daily Trust.

Daily Trust ta ruwaito yadda jirgin saman Air Peace, a ranar 13 ga watan Yuni, 2925, ya kutsa kai kan titin jirgin bayan ya sauka a filin jirgin saman Fatakwal, ɗauke da fasinjoji 103.

Jirgin ya kauce hanya daga titin jirgin ba tare da wani lahani ba.

Kauce hanyar jirgin sama kuskure ne ko rashin amfanin da izini na sanya jirgin sama ya kauce asalin titin jirgi.

Hukumar NSIB ta ce, “Jirgin yana aiki ne a matsayin jirgin sufuri na cikin gida da aka tsara daga Legas zuwa Fatakwal tare da mutane 103 a cikinsa, ya sauka a kan titin mai tsawo Runway 21 bayan rashin amfani da umarni, jirgin ya yi tafiya mai nisan mita 2,264 daga bakin titin inda ya tsaya ƙarshe a nisan mita 209 zuwa titin.

“Dukkan fasinjoji da ma’aikatan jirgin sun sauka lafiya, kuma ba a sami rahoton wani rauni ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fatakwal

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba