Aminiya:
2025-11-02@03:54:57 GMT

Budurwa ta mutu a ɗakin saurayin da ke shirin auren ta a Abuja

Published: 11th, September 2025 GMT

Wata budurwa mai shekaru 24 mai suna Kelechi Ebubechukwu, ta rasu a cikin wani yanayi da mai daure kai a gidan saurayinta da ke Gwagwalada, Babban Birnin Tarayya Abuja.

Wani ƙwararren masani kan tsaro, Zagazola Makama, ne ya bayyana hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Laraba.

A cewarsa, lamarin ya faru ne a ranar Talata.

Mota ɗauke da tabar wiwi ta yi hatsari a Kano, ta faɗa hannun jami’an NDLEA Likitoci sun bai wa gwamnati sa’o’i 24 kafin tsunduma yajin aiki 

Majiyoyin ’yan sanda sun ce binciken farko ya nuna cewa marigayiyar na fama da zazzabin cizon sauro kafin rasuwarta.

A cewar mjiyoyin, an samu takardar da ke dauke da rubutun magungunan da ake zaton na mai fama da cutar ne a dakin da lamarin ya faru.

Zagazola ya ce, “A ranar 9 ga watan Satumba, an samu rahoton wani lamari mai tayar da hankali na kisan kai a Gwagwalada, bayan wata mata mai shekaru 24 da aka gano sunanta Ebubechukwu Sunday Kelechi ta mutu ba zato ba tsammani a gidan saurayin da za ta aura.”

“Majiyoyi sun ce binciken farko na ’yan sanda ya nuna cewa tana fama da zazzabin cizon sauro kafin rasuwarta, kuma an samu magungunan cutar a wurin. Ba a ga wata alamar tashin hankali a jikinta ba.”

Makama ya kara da cewa an kama saurayin marigayiyar domin fadada bincike don gano ainihin musabbabin rasuwarta.

Lamarin Ebubechukwu dai ya kara yawan jerin matan da suka rasu a gidajen mazajensu ko samarinsu a cikin watannin baya-bayan nan a fadin Najeriya.

Rahotannin ’yan sanda sun nuna cewa yawancin irin wadannan abubuwan na faruwa ne yayin jima’i, yayin da wasu kuma ke da alaka da fada a tsakanin su ko kuma sanadiyyar tashin cututtukan da suke damun su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: budurwa Mutuwa Saurayi

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

 

Da yake sharhi game da wannan batu a wani rubutu da ya yi a Facebook a ranar Alhamis, Sheikh Gumi ya ce, Sanda ta yi matukar nadama kuma ya tabbata ba halinta ba ne irin wannan mugun aiki face aikin shaiɗan ne ya yi sanadiyyar iftila’in, ba don son ranta ba ne.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025 Manyan Labarai Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket
  • Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
  • Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi