Aminiya:
2025-11-02@08:42:50 GMT

Mota ɗauke da tabar wiwi ta yi hatsari a Kano, ta faɗa hannun jami’an NDLEA

Published: 11th, September 2025 GMT

Hukumar Hana da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kano, ta cafke buhuna uku da kuma sinki 150 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 112.

Bayanai sun ce an kama kwayoyin ne bayan wani hatsarin mota da ya faru a Gadar Tamburawa da ke kan hanyar Zariya zuwa Kano.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad-Maigatari, ya fitar a ranar Alhamis a Kano.

Likitoci sun bai wa gwamnati sa’o’i 24 kafin tsunduma yajin aiki  Tinubu ya bayar da umarnin a sake karya farashin kayan abinci

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 6:00 na safiyar ranar Asabar, lokacin da jami’an hukumar da ke sintiri suka ji karar hatsari tsakanin motar kirar Golf da wata babbar mota.

“Jami’anmu sun garzaya wurin don ceto mutanen da ke cikin motar Golf, inda suka cire gilashin gaban mota, taga da ƙofa don fitar da direban da fasinja,” in ji shi.

Ya kara da cewa fasinjan ya yi yunkurin tserewa lokacin da aka bude ƙofa, amma jami’an hukumar suka yi ram da shi.

“Binciken da aka yi a cikin motar ta Golf ya kai ga gano sinki 150 da buhuna uku na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 112,” in ji Muhammad-Maigatari.

A cewarsa, direban motar, wanda ke karbar magani a asibiti, ya amsa cewa shi ne wakilin wanda ya turo kayan, kuma ya taba kai irin wannan kaya a baya cikin Kano da wajen ta.

Muhammad-Maigatari ya kara da cewa direban ya amsa cewa ya bi hannun da ba nasa ba a titi don guje wa binciken NDLEA.

“Rahotannin farko sun nuna cewa direban babbar motar ya ji rauni mai tsanani. Abin da direban ya aikata ya kunshi laifuka biyu: bin hannun da ba nasa ba da ya janyo hatsari da kuma safarar miyagun kwayoyi,” in ji shi.

Jami’in ya ce hukumar karkashin jagorancin Kwamandan Jihar Kano, Abubakar Idris-Ahmad, za ta ci gaba da bin diddigin wadanda ke da hannu a safarar miyagun kwayoyin da nufin gurfanar da su a gaban kotu.

A ƙarshe, ya shawarci jama’a da su guji safarar miyagun kwayoyi, tare da bayar da rahoton duk wani motsi da bas u yarda da shi ba ke da alaka da miyagun kwayoyi ga hukumar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsari kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta raba zunzurutun kuɗi naira miliyan 63.4 ga iyalan jami’anta 84 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

Rundunar ta raba kudin ne a ƙarƙashin tsarin inshorar rayuwa da kuma tsarin kula da lafiyar iyali na Sufeto Janar na ’yan sanda.

 

An gudanar da rabon kuɗin ne a ranar Alhamis a Maiduguri babban birnin jihar kamar yadda Kakakin rundunar a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana a cikin wata sanarwa.

A cewar sanarwar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, wanda ya wakilci Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun, shi ne ya gabatar da takardun cakin kudin ga iyalan waɗanda suka ci gajiyar tallafin.

“Harkokin da suka shafi jami’anmu da iyalansu ya kasance babban fifiko ga rundunar,” in ji CP Abdulmajid yayin taron.

Ya ce wannan shiri na nuna tausayi da rikon amana, da kuma jagoranci mai nagarta daga Sufeto Janar wajen girmama jaruman da suka sadaukar da rayukansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyalan da suka amfana da tallafin da su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace, musamman wajen tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, da jin daɗin rayuwar iyalansu gaba ɗaya.

Ya yaba wa Sufeto Janar bisa ci gaba da tsare-tsaren jin daɗin jami’an rundunar, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyin da ke samar da agaji da kwanciyar hankali ga iyalan waɗanda suka rasa masoyansu.

A nata jawabin a madadin iyalan da suka amfana, Misis Nana Goni ta nuna godiya ga Sufeto Janar bisa goyon bayan da ya bayar, tana mai tabbatar da cewa za su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya kamata don inganta rayuwar iyalansu.

Rundunar ta bayyana cewa wannan rabon tallafi ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kula da walwala da mutuncin jami’anta da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya