Mota ɗauke da tabar wiwi ta yi hatsari a Kano, ta faɗa hannun jami’an NDLEA
Published: 11th, September 2025 GMT
Hukumar Hana da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kano, ta cafke buhuna uku da kuma sinki 150 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 112.
Bayanai sun ce an kama kwayoyin ne bayan wani hatsarin mota da ya faru a Gadar Tamburawa da ke kan hanyar Zariya zuwa Kano.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad-Maigatari, ya fitar a ranar Alhamis a Kano.
Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 6:00 na safiyar ranar Asabar, lokacin da jami’an hukumar da ke sintiri suka ji karar hatsari tsakanin motar kirar Golf da wata babbar mota.
“Jami’anmu sun garzaya wurin don ceto mutanen da ke cikin motar Golf, inda suka cire gilashin gaban mota, taga da ƙofa don fitar da direban da fasinja,” in ji shi.
Ya kara da cewa fasinjan ya yi yunkurin tserewa lokacin da aka bude ƙofa, amma jami’an hukumar suka yi ram da shi.
“Binciken da aka yi a cikin motar ta Golf ya kai ga gano sinki 150 da buhuna uku na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 112,” in ji Muhammad-Maigatari.
A cewarsa, direban motar, wanda ke karbar magani a asibiti, ya amsa cewa shi ne wakilin wanda ya turo kayan, kuma ya taba kai irin wannan kaya a baya cikin Kano da wajen ta.
Muhammad-Maigatari ya kara da cewa direban ya amsa cewa ya bi hannun da ba nasa ba a titi don guje wa binciken NDLEA.
“Rahotannin farko sun nuna cewa direban babbar motar ya ji rauni mai tsanani. Abin da direban ya aikata ya kunshi laifuka biyu: bin hannun da ba nasa ba da ya janyo hatsari da kuma safarar miyagun kwayoyi,” in ji shi.
Jami’in ya ce hukumar karkashin jagorancin Kwamandan Jihar Kano, Abubakar Idris-Ahmad, za ta ci gaba da bin diddigin wadanda ke da hannu a safarar miyagun kwayoyin da nufin gurfanar da su a gaban kotu.
A ƙarshe, ya shawarci jama’a da su guji safarar miyagun kwayoyi, tare da bayar da rahoton duk wani motsi da bas u yarda da shi ba ke da alaka da miyagun kwayoyi ga hukumar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO) ya ƙaryata zargin da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya yi masa, dangane da mutuwar wasu marasa lafiya sakamakon katse wutar lantarki da aka ce kamfanin ya yi.
Asibitin na AKTH ya bayyana damuwarsa a ranar Lahadi kan abin da ya kira abin takaici yana mai cewa mutanen da suka mutu za su iya tsira da ransu da ba a ɗauke wutar ba.
Amma a martanin da ya bayar, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama’a na KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce asibitin na ƙoƙarin ɓata sunan kamfanin ne kawai, domin an dawo da wutar tun kafin asibitin ya fitar da wannan sanarwar.
Sani ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga wani yunƙurin da ake yi na raba ginin asibitin da cibiyoyin lafiya daga gidajen ma’aikatan asibitin.
“Cibiyar asibitin da cibiyoyin lafiya suna da alaƙa da layin 33kV na Zariya Road wanda aka fi ba fifiko wajen raba wuta, kuma suna samun kimanin sa’o’i 22 na wutar lantarki a kullum ƙarƙashin tsarin Band A.
“Amma, shugabannin AKTH sun dage cewa sai gidajen ma’aikata sun ci gaba da kasancewa a layin wutar lantarki ɗaya da cibiyoyin lafiya. Wannan ya janyo barazana ga inganci da kwanciyar hankali na wutar da aka ware wa asibitin.
“An yi ƙoƙari sau da dama don raba gidajen ma’aikata daga cibiyoyin lafiya, amma haƙarmu ba ta kai ga cimma ruwa ba saboda ƙin amincewar shugabannin asibitin. Abin takaici, wannan ya haifar da matsala mai tsanani da ta janyo katsewar wutar da muke ƙoƙarin kaucewa,” in ji KEDCO.
Don tabbatar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga asibitin, kamfanin KEDCO ya ce yana ci gaba da aikin raba layukan wutar lantarkin biyu. Ya ce annan mataki ya zama dole don tabbatar da inganci, tsaro da kyautata lantarki ga asibitin.
Kamfanin ya kuma zargi asibitin da rashin biyan kuɗin wutar lantarki da gidajen ma’aikata ke amfani da ita, wanda ke shafar ingancin ayyukan samar da wuta na kamfanin.
KEDCO ya ce a cikin wata wasiƙa da ya aike ranar 12 ga Agusta, 2025, Babban Jami’in Kasuwanci na kamfanin, Muhammad Aminu Ɗantata, ya sanar da Shugaban Asibitin AKTH game da shirin dakatar da samar da wutar lantarki ga gidajen ma’aikata da wuraren da ba su da muhimmanci, sakamakon rashin cikakken biyan kuɗin wutar wata-wata.
Wasiƙar ta bayyana cewa:
“Duk da roƙon da aka yi sau da dama, asibitin ya ƙi biyan cikakken kuɗin wutar da yake sha a duk wata.
Wannan ya haifar da bashin wutar lantarki da ya kai ₦949,880,922.45 a watan Agustan 2025.
“An bukaci asibitin ya biya kuɗin watan Agusta 2025 na ₦108,957,582.29 gaba ɗaya cikin kwanakin aiki 10, don kaucewa yanke wuta a wuraren da abin ya shafa,” in ji wasiƙar.
Kamfanin ya ƙuduri aniyar ci gaba da samar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga AKTH a matsayin babbar cibiyar lafiya.
A ƙarshe, KEDCO ya roƙi shugabannin asibitin da su ba da haɗin kai a aikin raba layukan wutar, wanda ya ce yana da amfani ga marasa lafiya, ma’aikata, da al’umma baki ɗaya.