Aminiya:
2025-09-17@23:13:19 GMT

Matuƙin jirgin Air Peace na shan barasa, miyagun ƙwayoyi — Rahoton

Published: 12th, September 2025 GMT

Hukumar Binciken Hatsari ta Najeriya (NSIB) ta fitar da rahotonta na farko, inda ta tuhumi wani matuƙin jirgin sama na Air Peace da kuma wani ma’aikacin jirgin da laifin shan miyagun ƙwayoyi da barasa.

Masu binciken hatsarin sun gwada ma’aikatan jirgin cewa suna amfani da abubuwan da ake zargin su bayan da jirgin su da ya yi yunƙurin sauka tare da kauce hanya ba tare da izinin hakan ba a titin jirgin sama na filin jirgin sama na Fatakwal a ranar 13 ga Yuli, 2025.

’Yan Najeriya sun kusa fara shan wutar sa’o’i 24 babu ɗaukewa — Minista Likitoci sun tsunduma yajin aiki a fadin Najeriya

Hakan na ƙunshe ne a cikin wani rahoto na share fage mai ɗauke da sa hannun daraktan hulɗa da jama’a da taimakon iyali a hukumar NSIB, Madam Bimbo Olawumi Oladeji, wadda ta bayyanawa Daily Trust.

Daily Trust ta ruwaito yadda jirgin saman Air Peace, a ranar 13 ga watan Yuni, 2925, ya kutsa kai kan titin jirgin bayan ya sauka a filin jirgin saman Fatakwal, ɗauke da fasinjoji 103.

Jirgin ya kauce hanya daga titin jirgin ba tare da wani lahani ba.

Kauce hanyar jirgin sama kuskure ne ko rashin amfanin da izini na sanya jirgin sama ya kauce asalin titin jirgi.

Hukumar NSIB ta ce, “Jirgin yana aiki ne a matsayin jirgin sufuri na cikin gida da aka tsara daga Legas zuwa Fatakwal tare da mutane 103 a cikinsa, ya sauka a kan titin mai tsawo Runway 21 bayan rashin amfani da umarni, jirgin ya yi tafiya mai nisan mita 2,264 daga bakin titin inda ya tsaya ƙarshe a nisan mita 209 zuwa titin.

“Dukkan fasinjoji da ma’aikatan jirgin sun sauka lafiya, kuma ba a sami rahoton wani rauni ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fatakwal

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar