Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Published: 12th, September 2025 GMT
Akpabio ya yi kira ga duk ƙasashen membobin WAAPAC da su samar da izinin majalisa ga kwamitocin da suka dace, yana mai cewa hakan zai tabbatar da ‘yancinsu da ingancinsu wajen kare dukiyar jama’a.
“Bashin gwamnati, idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai zama aiki ne mai muhimmanci wajen ɗaukar nauyin ci gaba, ayyukan more rayuwa, da ci gaba mai ɗorewa.
Wannan shi ya sa majalisa ba za yi watsi da sanya ido a kansa wajen bashi kulawa ba.
“Kwarewar Nijeriya ta nuna cewa idan kwamitocin majalisa suka samu ikon doka, gaskiya da riƙon amana sun ƙaru, kuɗi ya yi ƙarfi, to dimokuraɗiyya ta ƙara inganci,” in ji shi.
A nasa ɓangaren, Abbas ya gargaɗi cewa basussukan Nijeriya sun kai wani matsayi mai hatsari, inda ya buƙaci majalisun dokoki a faɗin Yammacin Afirka su ƙarfafa sa ido kan aro na gwamnati domin kare makomar ‘yan ƙasashensu.
Da yake magana a madadinsa, Jagoran Majalisar Wakilai, Hon. Julius Ihonɓbhere, Abbas ya bayyana cewa jimillar basussukan gwamnatin Nijeriya ya kai Naira tiriliyan 149.39 (kimanin Dalar Amurka biliyan 97) a zangon farko na shekarar 2025, wanda ya nuna ƙaruwar ta yi tsanani daga Naira tiriliyan 121.7 a shekarar da ta gabata.
Ya bayyana damuwa kan matsayin bashin da aka kwatanta da GDP, wanda a halin yanzu ya kai kusan kashi 52 cikin 100, sama da iyakar kashi 40 cikin 100 da doka ta ƙayyade.
Ya ce: “Wannan karya haddin bashi ne luma hakan wata alama ce ta matsin lamba ga ɗorewar tattalin arziki. Hakan ya nuna gaggawar buƙatar ƙarfafa sa ido, yin aro cikin gaskiya da bayyana dukkan bayanai, da kuma samun haɗin kai domin tabbatar da cewa kowace Naira da aka aro ta samar da ainihin amfanin tattalin arziki da zamantakewa.
“A duk faɗin Afirka, matakin bashi ya kai wani mummunan matsayi. A shekarar 2022, jimillar bashin ƙasashen nahiyar ya kai Dala tiriliyan 1.8, inda bashin wajen shi kaɗai ake sa ran zai zarce Dala tiriliyan 1 a shekarar 2023.”
Ya ce: “Ƙasashe da dama yanzu suna cikin mummunan yanayi na cin bashin da aka kwatanta da GDP: misali; Sudan na da kaso 344, Angola kaso 136.8, Ghana 84, Kenya kusan 70, yayin da Afirka ta Kudu ta haura kaso 77.”
Kakakin majalisar ya lura cewa a faɗin Afirka, bashi ya zama matsalar tsarin tattalin arziki, inda ƙasashe da dama ke kashe kuɗi fiye da na kula da lafiya da sauran muhimman ayyuka wajen biyan bashin da suka karɓa.
A cewarsa, kashi 35 na bashin na ƙasashen Turai ne na masu ba da rance masu zaman kansu, kashi 39 na ƙungiyoyin haɗin gwiwa irin su IMF da Bankin Duniya, kashi 13 kuma na ƙasashen da ke bayar da rance kai tsaye (bilateral creditors), sannan kashi 12 daga Ƙasar China.
Abbas ya ce Nijeriya ta ƙuduri aniyar jagorantar kafa tsarin duba bashin ƙasashen Yammacin Afirka ta majalisar dokoki ƙarƙashin WAAPAC, domin daidaita rahotannin bashi, samar da ƙa’idojin yanki kan gaskiya da bayyana bayanai, tare da bai wa majalisu damar samun bayanai cikin lokaci don inganta bincike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
Sanata Sunday Marshall Katung, wanda ke wakiltar mazabar Kaduna ta Kudu a majalisar dattawa, ya sanar da hukuncin da ya yanke na komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yana mai cewa wannan mataki ne da ya dace domin inganta aikin wakilci da kuma tabbatar da ƙarin haɗin kai ga al’ummar mazabarsa.
A cikin wata sanarwa mai taken “Sabon Babin Rayuwa: Saƙon Haɗin Kai da Manufa Ɗaya,” Sanata Katung ya bayyana cewa wannan shawara ta biyo bayan dogon shawarwari da aka yi da mazauna mazabarsa, jagororin siyasa, iyalansa da abokan aikinsa.
Ya ce, “Wannan sauyin matsayi yana fitowa ne daga niyyar gaskiya ta yin wa mutanenmu hidima cikin inganci, da tabbatar da cewa muryarmu tana da ƙarfi kuma ana jin ta a manyan teburan yanke shawara da ke tsara makomar al’ummarmu.”
Ya ƙara da cewa wannan mataki ya zama dole ne bayan kiraye-kirayen da aka yi daga sassa daban-daban na mazabarsa, tare da yabawa irin sha’awar da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, suka nuna wajen yin aiki tare da shi domin kawo “ci gaba mai tarihi da ban mamaki” a yankin.
Sanata Katung, yayin canza shekan tare da Hon. Daniel Amos da wasu abokansa a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, ya nuna gamsuwa da “ayukan ci gaban” jam’iyyar APC a yankin Kaduna ta Kudu, yana mai cewa suna nuna adalci, daidaito, da ci gaba.
Ya ce, “Zamanin warewa da nuna bambanci, musamman a baya-bayan nan, yana gushewa, kuma ana maye gurbinsa da gwamnatin da ke da manufa da haɗin kai.”
“Saboda haka muna matsawa gaba domin tabbatar da cewa waɗannan nasarori sun dore kuma sun yadu zuwa sauran al’ummomi da dama a yankin,” in ji shi.
Sanatan ya kuma roƙi abokai da abokan aiki da ba su goyi bayan wannan mataki nasa ba, da su mutunta ra’ayoyi daban-daban, tare da kaucewa barin siyasa ta kawo rarrabuwar kawuna a tsakaninsu.
Ya ambaci kalmar Thomas Jefferson da cewa, “Ban taɓa ɗaukar bambanci a ra’ayi na siyasa, addini ko falsafa a matsayin dalilin janye ƙauna daga aboki ba.”
“A tare, mu ci gaba da zama ɗaya a manufa, mu dage da fata, kuma mu mai da hankali wajen samar da makoma mafi kyau ga al’ummar Mazabar Kaduna ta Kudu.”
Sanata Katung ya tabbatar da ƙudurinsa na ci gaba da aiki don haɗin kai da cigaba.
Daniel Karlmax