Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi
Published: 12th, September 2025 GMT
Masanan sun yi gargaɗi yayin da Shugaba Bola Tinubu ya sake tabbatar da ƙudurin gwamnatinsa na sake fasalin ɓangaren lafiya na Nijeriya, inda ya bayyana cewa babu wani ɗan ƙasa da ya kamata ya rasa rayuwarsa saboda rashin wutar lantarki a cibiyoyin lafiya.
Yayin da yake jawabi a Taron Tattaunawar Masu Ruwa da Tsaki na Ƙasa kan Wutar Lantarki a Ɓangaren Lafiya, a Ladi Kwali Hall na Continental Hotel, Abuja, Shugaban ƙasa, wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya wakilta, ya lura cewa rashin wutar lantarki da ke ci gaba a asibitoci na rage ingancin kulawa da kuma jawo asarar rayuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
Gwamnan Jihar Borno, Umara Zulum ya sanar da fara fitar da kayayyakin robobi zuwa ƙasashen duniya wanda hakan ke nuna wani gagarumin ci gaba a wani ɓangare na ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arzikin Jihar.
Gwamnan ya jaddada cewa, wannan matakin wani ɓangare ne na babbar ajanda na bunƙasa masana’antu da kuma kawar da dogaro da jihar kan yi na kason da gwamnatin tarayya ke bayarwa duk wata.
Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a EkitiZulum ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis yayin rangadin duba masana’antar robobi ta Borno da ke cikin yankin masana’antu na Maiduguri.
“Ina farin cikin lura cewa mutanen Jihar Borno ba za su sake sayen kayan robobi daga wasu wurare ba, kun ga an sayar da kayayyakin ga ƙasashen maƙwabta da sauran jihohi a cikin Najeriya.”
“Za mu zuba jari sosai a masana’antunmu, don haka nan gaba kaɗan, gwamnatin Jihar Borno ba za ta sake dogara da asusun tarayya ba don ayyukanta na yau da kullum,” in ji Zulum.
Gwamnan ya bayyana cewa masana’antar ta fara fitar da kayayyakinta ga ƙasashen waje, tare da jigilar kayayyakin filastik da aka gama zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Chadi da Jamhuriyar Kamaru.
Zulum ya lura cewa an fara gina cibiyar ne a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Kashim Shettima, amma an farfaɗo da ita a matsayin wani ɓangare na shirin murmurewa da ci gaban gwamnatinsa.