Leadership News Hausa:
2025-09-17@20:28:28 GMT

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Published: 2nd, September 2025 GMT

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da ajandar mulkin duniya a taron “SCO+” na birnin Tianjin a jiya Litinin. Wannan ajanda, ta nuna hanyar da za a bi, tare da ba da jagoranci ga aiwatar da ayyukan gina tsarin mulkin duniya mai adalci da dacewa, a karkashin yanayin duniya mai fuskantar manyan sauye-sauye, da kuma jagorancin cike gibin kudi na samar da ci gaba da bunkasa.

Sabuwar ajandar mulkin duniya da Xi Jinping ya gabatar, ta yi magana kai tsaye kan wasu muhimman abubuwa guda uku a tsarin jagorancin duniya, wato rashin daidaiton iko, da rarrabuwar ra’ayoyi, da kuma rashin daukar matakai.

Ajandar, wadda ta fitar da wasu ka’idoji guda biyar, wato tabbatar da daidaiton ikon mulkin kasa, da bin dokokin kasa da kasa, da aiwatar da ra’ayin bangarori daban-daban, da ba da shawarar kula da bukatun jama’a, da kuma mai da hankali kan aiwatar da matakai na samar da wata hanya a fayyace ga kasashen duniya ta gudanar da ayyuka cikin adalci, yayin da ake jagorancin duniya, kamar shiga ayyuka, da yanke shawara da kuma samun fa’ida.

Misali, ajandar ta jaddada cewa, “Akwai bukatar inganta wakilci da murya tsakanin kasashe masu tasowa,” wannan hakan ya dace da fatan kasashe masu tasowa na samar da tsari mai adalci. Kazalika, shawarar “Kaucewa amfani da ma’aunai biyu, wato kauracewa kakaba ‘dokokin gida’ na wasu kasashe a kan sauran kasashe”, wanda hakan ya nuna rashin amincewa da ra’ayin bangare guda daya. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Tun daga ranar 18 ga wata, za a kaddamar da fim mai taken 731 a sassan duniya da dama, fim din da ya bayyana yadda rundunar sojojin kasar Japan da suka kutsa kasar Sin suka gudanar da nazari a kan hada makamai da cututtuka tare da gudanar da gwaje-gwaje a jikin al’ummar kasar Sin, a birnin Harbin na lardin Heilongjiang da ke arewa maso gabashin kasar Sin, kafin al’ummar kasar Sin su cimma nasarar yaki da su.

 

A ranar 19 ga watan Agusta, hukumar kula da tsaron kasar Rasha ta fitar da wata takardar sirri da yanzu gwamnati ta mayar da ita ba ta sirri ba, wadda ta nuna cewa, domin neman yin amfani da makaman da aka hada da cututtuka a yakin kutsen da suka kaddamar a kasar Sin, reshen rundunar sojojin Japan da suka yi kutse a kasar Sin mai lambar 731, sun yi ta gudanar da gwaje-gwaje a jikin al’umma, har ma sun kai harin boma-bomai da aka samar da cututtuka a kan daruruwan Sinawa, don neman tantance ingancin cututtuka ta hanyar kirga mutanen da suka harbu da cututtuka.(Lubabatu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
  • Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya