Leadership News Hausa:
2025-11-02@06:26:20 GMT

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Published: 31st, August 2025 GMT

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Matsala ta farko na yi mata take da:

1. Sai Bango Ya Tsage….: Gaskiyar diyan Bawo, da yake cewa, ‘Sai bango Ya tsage, kadangare ke samun wurin shiga. Lallai babu yadda za a yi gwamnati da sauran manyan al’umma suna kallon harshen Hausa a matsayin wani harshe wanda nazartarsa koma baya ne ga al’umma kuma a samu wannan harshen ya ci gaba da yaduwa kamar wake dan arba’in.

An taba yin wani shugaban kasa da ya ayyana nazartar wasu darussa a matsayin bata lokaci domin bai ma san a ina za su yi aiki ba. Duk kuwa da kasancewar duk kasar da ya ratsa a Arewacin kasar domin yakin neman zabe, da harshen Hausa yake magana.

Abin da nake nufi a takaice, gwamnati ta yi watsi da harkar koyo da koyarwar harshen Hausa, domin a ganinta ba shi da amfani, wannan ne ya sa har harshen Yarabanci wanda ko kwalar harshen Hausa bai kai ba a wajen tara manyan manazarta kama daga Farfesoshi da kuma yawan gidajen yada labarai da jaridu da makarantun duniya wadanda suke amfani da harshen Hausar ba.

Kadan daga cikin gudunmuwar da gwamnati ta bayar wurin ci bayan nazarin harshen Hausa sun hada da: a. Mayar da karatun Hausa a matakin sakandare ZAbI. b. Tsaurara matakin neman gurbin karatun jami’a domin karantarsa da JAMB suka yi. c. Rashin bayar da tallafin karatu domin nazartar harshen kamar yadda sauran harsuna da kuma gwamnatoci ke yi a wasu darussan. Da sauransu da yawa.

 

Na sa wa batu na biyu taken:

2. Ka ki Naka, Duniya Ta So Shi: Hakika da yawan al’ummar Hausawa ba sa alfahari da harshen Hausa musamman ta fannin zuwa su nazarci harshen kamar yadda Turawa da Larabawa ke nazartar nasu harsunan, duk kuwa da irin tasirin da hakan yake da shi a rayuwa bakidaya. Amma a haka sai ka iske kasashen waje sun dage wajen gabatar da rubuce-rubuce da yada harshen ta kafafe mabambanta har ma da karantar da shi a manyan jami’o’in duniya. Amma mu a nan kallon uku aho ake yi wa da yawan wadanda suke nazartar Hausa. Abin takaicin masu wannan dattin kwakwalwar kuma su ne za ka tarar a kaso 90 na rubututtukansu a shafukansu na sada zumunta da Hausa suke yi, idan suna koyon littafan addini duk sai an fassara masu da Hausa ko da kuwa da wane irin harshe aka rubuta littafin addinin nan, ko ka san batan bakatantan!

Abin dariya abin tausayi, wai kunama ta harbi dan tsako. Yanzu bai zamo abin kunya ba, a ce kasa kamar Nijar wadda masu magana da harshen Hausar kasar ba su kama kafar rabin na Arewacin Nijeriya ba, amma a ce kasar sun ayyana harshen a matsayin harshen kasa. Me ya sa gwamnatocin Arewa ba za su ayyana shi a matsayin harshen Arewacin kasar ba, idan ana tokabon kasar bakidaya tana da manyan harsuna guda 3?

Har wa yau, wasu daga cikin malamai suna bayar da gudummuwa wajen kin nazartar wannan harshe, musamman ta fuskar yadda suke mu’amalantar dalibansu musamman ta fuskar kwauron maki da bayar da wahala yayin bincike na ba gaira babu dalili, wanda a hasashena ba komai yake kawo haka ba, sai don kawai a razana ka, wanda hakan ne ya razana da yawa suka kauracewa nazartar harshen.

 

Batu na uku na yi masa ishara da:

3. Idan An Bi Ta barawo.. Lallai malamai da daliban harshen ya kamata su ci gaba da ayyukan da na san an faro da dadewa na fassarar muhimman kalmomi na fannonin ilimi da dama, wanda hakan shi zai ba wa masu nazartar harshen dama wajen kutsawa kowane fanni da yin kaka-gida wajen fito wa da dalibai abubuwan a sarari domin saukaka fahimtar darussan. Kamar yadda sauran harsunan duniya irin su: Larabci da Turanci da Indiyanci da Sinanci (Chinese) da sauransu, suka yi.

 

Gudummuwar Harshen Hausa.

Ido ba mudu ba, amma ya san kima. Ga kadan daga cikin wasu gudunmuwar da harshen yake bayarwa a takaice:

1. Babu wani littafi na addini da ake karantarwa a kasar nan wanda ba a fassara ba ko ake yunkurin fassara shi zuwa harshen Hausa.

2. An fassara da yawan littattafan kimiyya da na Lugga da na lissafi hada har da na tarihi da sauransu domin ci gaban al’umma.

3. Babu wata kafar sadarwa da harshen Hausa bai yi zarra a cikinta ba, kama daga Instagram da Tiktok da WhatsApp da D (Twitter) har ma da uwa uba Facebook.

Haka nan, Harshen Hausa shi ne ya mamaye kafafen yada labarai na Amuruka da Sin da Faransa da sauransu. Bar batun jaridu da kullum ake fito da su cikin harshen domin nusar da al’umma halin da duniya ke ciki.

4. Bugu da kari, Manazarta sun samar da kundayen bincike na falsafa da al’ada hadi da adabi da ma harshe. An kuma rubuta manya da kananan littattafai wadanda ba wanda ya isa ya fadi adadinsu da irin fannonin da littattafan suka tabo. Ana kuma samar da mukaloli a fagage mabambanta ba don komai ba sai don kokarin ciyar da harshen da kasa da kuma al’umma gaba.

 

SHAWARWARI:

Akwai matakai da yawa da ya kamata a dauka domin dawo da martabar koyon wannan harshe mai albarka. Ga kadan daga ciki:

1. Tafiya da zamani.

2. Saukaka hanyoyin koyo da koyarwa.

3. Mayar da nazarin harshen wajibi a kananan makarantu na firamare da sakandire.

4. Sanya koyon shi ya zama wajibi ga duk dalibin kasar waje da ya zo yin karatu a kasar nan, kamar yadda da yawan kasashe suke yi.

5. Kutsawa fannonin kimiyya da fasaha da fannin likitanci da magunguna domin ci gaba da gudanar da nazarce-nazarce.

6. Sanya shi a cikin darussan dole Gens/GSE manhajar koyarwar jami’o’i da kwalejojin ilimi da na kimiyya.

7. Mayar da harshen Hausa ya zamo harshen hukuma a yankin Arewa idan ma ba kasar (Nijeriya) duka bakidaya ba.

8. karfafa gwiwar iyaye da ta abokai har ma da uwa uba malamai ga masu nazarin harshen Hausa.

9. A aje kwarya a burminta. Ka da a dauki aikin da aka san manazarcin harshen Hausa ne kadai zai iya a danka shi ga wani, musamman abin da ya shafi ayyukan fassara da na talife-talife.

Aiwatar da wadannan da ma wasu abubuwa za su taimaka gaya wajen ganin an dawo da kima da kuma martabar nazarin harshen Hausa.

 

Kammalawa:

A takaice wannan takarda ta tattaro wasu bayanai ne da suka shafi matsalolin da harshen Hausa yake fuskanta wadanda suka haddasa mashi koma baya, da kuma gudummuwar da harshen Hausar yake bayarwa a zamanace da addini da ma rayuwa bakidaya, daga karshe kuma takardar ta bijiro da wasu hanyoyi da za a bi domin ganin an dawo da martabar nazartar harshen a kasa bakidaya.

Jikamshi, ya rubuta albarkaci bikin Ranar Hausa ta Duniya ta bana da aka yi bikinta ran 26/08/2025

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da harshen Hausa nazartar harshen nazarin harshen kamar yadda da sauransu

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

 

Xi ya kuma bayyana cewa, saboda bambancin yanayin kasashen Sin da Amurka, ba makawa akwai wasu sabanin ra’ayi, amma baya ga kalubale da takara, ya kamata shugabannin biyu su rike shugabanci, da kuma samar da alkibla mai dacewa, don ba da damar bunkasa dangantakar Sin da Amurka ta ci gaba da tafiya cikin kwanciyar hankali.

 

A nasa bangare, Trump ya ce, yana farin ciki matuka bisa haduwa da dadadden abokinsa. Ya ce, “Za mu tattauna da mai girma shugaban kasar Sin Xi Jinping. Ina da imanin cewa, mun riga mun kai ga cimma matsaya daya, kuma za mu cimma karin matsaya a nan gaba. Xi Jinping wani sahihin shugaba ne mai kima.”

 

Ya kuma ce, “Ba shakka kasashen biyu za su kafa nagartacciyar hulda ta dogon lokaci, ina kuma farin cikin hakan tare da shugaba Xi.”

 

Shugabannin biyu sun shafe sa’a 1 da mintuna 40 suna tattaunwa.

 

A wannan rana kuma, shugaban kasar Xi Jinping ya isa kasar Korea ta Kudu, domin halartar taron kwarya-kwarya na shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Asia da Pasifik (APEC) karo na 32, bisa gayyatar da shugaban kasar Korea ta Kudu Lee Jae-myung ya yi masa.(Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II October 30, 2025 Manyan Labarai Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik October 29, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai