Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:15:25 GMT

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

Published: 29th, August 2025 GMT

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Labour Party a 2023, Peter Obi, ya soki gwamnatin tarayya kan ƙarin kuɗin fasfo da aka sanar cikin makon nan. Ya bayyana cewa wannan ƙarin ya nuna rashin la’akari da halin da talakawa ke ciki a yau.

A cewar Obi, sabon farashin fasfo na – ₦100,000 mai shafuka 32 da ₦200,000 mai shafuka 64 – ya fi sabon albashin ƙasa na ₦70,000, abin da ya ce bai dace ba da halin da ma’aikata ke ciki.

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Ya zargi gwamnati da ƙara ƙaƙabawa jama’a ƙarin nauyi maimakon sauƙaƙa musu, musamman a lokacin da tattalin arziƙin ƙasa ke cikin matsala.

Obi ya yi kira ga gwamnati da ta sake duba lamarin, yana mai cewa abin da al’umma ke buƙata a yanzu shi ne manufofin da za su rage wahala, ba ƙara tsawwala taɓarɓarewar rayuwa ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.

Ministan Noma  Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta  Jihar Jigawa.

 

Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.

Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.

Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na  zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.

Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.

Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja