Aminiya:
2025-12-13@13:07:42 GMT

Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki

Published: 19th, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakan da suka dace domin ganin cewa garin Marte bai koma hannun ’yan Boko Haram ba.

Zulum, ya kai ziyara garin Marte domin duba halin da ake ciki da kuma yadda za a tabbatar da zaman lafiya.

Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su Yadda Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5

Kafin zuwansa, ’yan ta’adda sun sake karɓe iko da Marte bayan harin da suka kai a ranar Juma’a, inda mutane da dama suka tsere zuwa garin Dikwa.

Gwamnan, ya ce mutane kimanin 20,000 ne suka tsere daga Marte, wanda hakan ka iya kawo matsala musamman ga matasa da za su iya shiga cikin harkokin ta’addanci.

Ya ce: “Muna da alhakin kare Marte. Idan muka rasa wannan gari, za mu iya rasa sauran ƙananan hukumominmu.

“Don haka ina roƙon Gwamnatin Tarayya da sojojin Najeriya su haɗa hannu wajen kare wannan gari.”

Zulum, ya kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro domin kawo zaman lafiya mai ɗorewa a Jihar Borno.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Ɗauki Gwamnatin tarayya hari Marte

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno

Wani kwalekwale da ke ɗauke da fasinjoji takwas ya kife yayin da yake ƙetare kogin da ke kan iyaka da garin Gamboru na Najeriya da Fotokol a ƙasar Kamaru, inda mutane uku suka mutu.

Lamarin ya faru ne da misalin qarfe 6:30 na yamma lokacin da kwalekwalen, wanda wani Mamman Nur Abbagana na Kasuwan Katako, Gamboru ke tuƙa shi ya kife a tsakiyar ruwa tare da jefa dukkan fasinjoji cikin ruwa.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa dukkan fasinjoji takwas ’yan ƙasar Chadi ne da ke tafiya daga Jos, Jihar Filato, a kan hanyarsu ta zuwa N’Djamena, Jamhuriyar Chadi.

An ceto fasinjoji biyar, waɗanda aka tabbatar da suna raye ba su mutu ba.

Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA

Wata mata mai suna Alphosine Makebu Beboroum, mai shekaru 34, da ’ya’yanta mata biyu Centich Mamajibe, mai shekaru 3, da Mamajilem Bebaroum, ‘yan watanni 10, sun nutse kuma har yanzu ba a gano su ba har zuwa Kammala wannan rahoto, duk da ana cigaba da gudanar da aikin ceto da bincike.

A halin yanzu, hukumomin ’yan sanda sun kuma tabbatar da kama mai tuƙa kwale-kwalen saboda karya umarnin gwamnatin Jihar Borno na tilasta wa duk masu aikin kwalekwale da su yi amfani da jakar ceto.

Kakakin rundunar ASP Nahum Kenneth Daso ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu