Aminiya:
2025-11-02@06:26:21 GMT

Ambaliya: NEMA ta raba kayan tallafi a Yobe 

Published: 31st, August 2025 GMT

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta raba wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Ƙaramar Hukumar Potiskum ta Jihar Yobe, kayan tallafi.

Darakta Janar na hukumar, Zubaida Umar, ta amince da fara wannan tallafi a Potiskum, inda ta samu wakilcin Abdullahi Garba, ko’odinetan ofishin NEMA na Maiduguri.

An kama direban mota da jabun kuɗin N1m a Oyo Mutum 13 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Zamfara 

A cewarta, wannan mataki ya biyo bayan ambaliyar ruwa da ta auku a ranar 15 ga qatan Agusta, 2025.

Ambaliyar ta shafi dubban jama’a kuma ta lalata gidaje da dama.

Binciken da NEMA tare da wasu ƙungiyoyin agaji suka gudanar ya nuna cewa gidaje 2,557 ne abin ya shaf, inda wasu suka rushe baki ɗaya.

Wuraren da ambaliyar ta fi shafa sun haɗa da tsohon gidan yari, Filin Mashe, Unguwar Makafi, Unguwar Jaje, Tsangaya, Rugan Fulani, da Bayan Sabon Gidan Yari.

Zubaida, ta bayyana cewa rabon kayan agaji kamar abinci, kayan masarufi, da kayan gini na nufi rage wa jama’a raɗaɗin da iftila’in da ya same su.

Ta ƙara da cewa: “Wannan mataki ya nuna cewa NEMA da abokan hulɗarta suna da niyyar taimaka wa al’umma domin rage musu raɗaɗin da ya faru.”

Hukumar ta yi rabon kayan ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) da kuma hukumomin tsaro a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa kayan tallafi

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025 Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Matashi ya rasa ransa a kan soyayya a Yobe