Har ila yau, hukumar jiragen kasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa; an fara bincike kan hatsarin da jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna ya yi a garin Asham da ke Jihar Kaduna.

 

Hukumar ta ce, binciken zai gudana ne karkashin kulawar hukumomin da abin ya shafa tare da sa ido daga ma’aikatar sufuri ta tarayya, domin kokarin gano musabbabin faruwar al’amarin.

 

A cikin sanarwar da NRC ta fitar a yammacin ranar Talata, ta bayyana cewa; jimillar mutum 618 ne suke cikin jirgin a lokacin da ya sauka daga kan hanyarsa.

 

Kazalika, hukumar ta bayyana cewa; daga cikin fasinjojin, mutum akalla 14 ne suka samu raunuka daban-daban, sannan kuma an garzaya da su asibiti. Sauran fasinjojin kuma, an mayar da su zuwa tashoshin Idu da Kubwa cikin wani jirgi da aka turo daga Abuja.

 

Haka kuma, an dakatar da dukkanin ayyuka da zirga-zirgar jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna na dan wani lokaci, har sai an kammala bincike da kuma gyara hanyar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp ShareTweetSendShare Previous Post Ranar Hausa: Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya Related Manyan Labarai Ranar Hausa: Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya 59 minutes ago Labarai Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa 9 hours ago Labarai Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya 10 hours ago Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya  12 hours ago Labarai Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna 13 hours ago Manyan Labarai Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru  14 hours ago

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Babban sakataren MDD António Guterres, ya bayyana a jiya Talata cewa, jerin shawarwarin da Sin ta gabatar wato shawarar raya duniya, shawarar tabbatar da tsaron duniya, shawarar raya wayewar kan al’ummun duniya, da kuma jagorantar harkokin duniya, sun dace da ka’idar kundin tsarin MDD.

Guterres ya bayyana hakan ne yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida a wani taron manema labarai da aka yi a ranar. Ya ce shawarwarin da Sin ta gabatar sun mutunta manufar kasancewar bangarori da dama, kuma sun goyi bayan MDD a matsayin cibiyar hadin gwiwar kasa da kasa, tare da dukufa kan inganta hadin gwiwa tsakanin kasashe daban daban da warware rikice-rikice cikin lumana.

Guterres ya kara da cewa, yanzu ana fuskantar rarrabuwar kawuna a fagen siyasa ta duniya da kuma karuwar yaduwar rikice-rikice, da ma rashin hukunta masu laifi. Bugu da kari, sabbin fasahohi suna ci gaba da bullowa “ba tare da bin wani tsari ba”, yayin da rashin daidaito ke kara tsananta. A wannan yanayi, babban taro karo na 80 na MDD mai tsawon mako guda da za a fara a mako mai zuwa, zai ba da duk wata dama ga tattaunawa da shiga tsakani.(Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara