Gwamnatin Gombe da Rotary sun yi shirin rage mutuwar mata da yara
Published: 28th, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Gombe tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Rotary International sun ƙaddamar da shirin aikin jinya domin rage mace-macen mata da yara a faɗin jihar.
Shirin da aka gudanar a Ƙananan hukumomi uku da suka haɗa: Gombe da Kaltungo da Yamaltu-Deba, inda aka yi wa jama’a gwaje-gwaje, jinya da wayar da kai a unguwannin Yelenguruza da Kagarawal.
Shugaban Rotary Reproductive, Maternal and Child Health a Nijeriya, Farfesa Emmanuel Adedolapo Lufadeju, ya bayyana cewa fiye da mutum 120 aka duba a unguwar Kagarawal kaɗai, inda aka samu kashi 70 cikin 100 sun kamu da zazzaɓin cizon sauro.
Ya ce, tun daga shekarar 2013 Rotary ke gudanar da irin wannan shiri a sassa daban-daban na ƙasar, kuma ya bayyana na Gombe a matsayin ta daban wanda aka gudanar a wurare biyu lokaci guda.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Habu Dahiru ya yaba wa Rotary bisa haɗin gwiwa tare da kira ga jama’a su riƙa cin moriyar asibitocin da gwamnati ta sabunta a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.
Ya shawarci mata masu juna biyu da su riƙa zuwa duba lafiya a asibiti, kana iyaye su tabbatar da yin allurar rigakafi ga ‘ya’yansu ’yan ƙasa da shekara biyar domin kare su daga mutuwa marar dalili.
Wasu daga cikin al’ummar da suka ci gajiyar shirin a Unguwar Kagarawal sun nuna farin ciki da godiya ga gwamnati da abokan haɗin gwiwa bisa kawo musu tallafin jinya a kusa da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gombe da Kaltungo da Yamaltu Deba
এছাড়াও পড়ুন:
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya (NUT) reshen Jihar Gombe, ta ziyarci shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi na jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, a ofishinsa da ke Gombe.
Shugaban ƙungiyar, wanda shi ne shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, ya bayyana cewa gwamnati da shugabannin ƙananan hukumomi za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen inganta walwalar malamai.
Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyiYa ce: “Ba za mu taɓa barin malamai su shiga cikin matsanancin hali ba. Za mu duba matsalolinsu domin tabbatar da walwalarsu da ci gaban ilimi a jihar.”
Sani, ya kuma yaba da yadda NUT ke tattaunawa cikin lumana da kawo shawarwari maimakon ɗaukar matakan da za su iya kawo tsaiko ga harkar ilimi.
A nasa jawabin, shugaban NUT na jihar ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna matsalolin da malamai ke fuskanta, musamman na makarantun firamare da ƙananun sakandare da ke ƙarƙashin kulawar ƙananan hukumomi.
Ya ƙara da cewa manufar NUT ita ce samar da fahimtar juna da haɗin kai tsakaninsu da shugabannin ƙananan hukumomi domin gano hanyoyin magance matsaloli cikin lumana.