Gwamnatin Kano ta musanta karkatar da N6.5bn daga baitul-malin jihar
Published: 25th, August 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta musanta rahotannin da ke zarginta da karkatar da Naira biliyan 6.5 daga baitul-malin jihar, tana mai cewa labarin “ƙarya ne da ‘yan adawa suka kitsa domin ɓata mata suna.”
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na Gwamnatin Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Litinin.
Sanarwar ta ce labarin da aka wallafa a wani shafin yanar gizo a ranar 22 ga watan Agusta, wani yunƙuri ne na ɓata sunan gwamnatin da kuma lalata martabar jami’anta kafin Zaɓen 2027.
Sanarwar ta ce taƙaddamar wadda a yanzu haka tana gaban kotu ta shafi Babban Darektan Tsare-Tsare (DG Protocol) na Gidan Gwamnati, Abdullahi Ibrahim Rogo, inda ta jaddada cewa nauyin da aka ɗora wa ofishinsa aiki ne na gudanarwa kawai kuma ba shi da ikon riƙon kuɗaɗen gwamnati kai tsaye.
“Dukkan kuɗaɗen da ake fitarwa zuwa ma’aikatu da hukumomi ana yin su ne bisa kasafi da tsarin kuɗin gwamnati.
“Babu wani mutum da ke riƙe kuɗin ma’akatu, hukumomi ko cibiyoyin gwamnati ba tare da dalilin da aka ware masa ba,” in ji sanarwar.
Gwamnatin ta bayyana cewa Ofishin Protocol aikinsa ya haɗa da shirya jigilar gwamnati, walwala da jin daɗi, masauki, tafiye-tafiyen gwamna da kuma karɓar baƙi, ciki har da jakadu da manyan baƙi. Kuma saboda irin nauyin da yake ɗauka, ofishin kan sarrafa manyan kuɗaɗe amma ƙarƙashin amincewar gwamna ne kacokam.
Sanusi Bature ya ce gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta jajirce wajen gaskiya, riƙon amana da adalci, kuma ba za ta yarda a zubar da mutuncin jami’anta ta hanyar wata farfaganda ba.
Ya zargi jam’iyyun adawa da suka ɗauki hayar masu ƙirƙirar ƙorafe-ƙorafe da yaɗa bayanan ƙarya kan jami’an gwamnatin NNPP.
Sanarwar ta kuma tunatar da yadda gwamnatin baya ƙarƙashin Abdullahi Ganduje ta kashe fiye da N20bn ta hannun Ofishin Protocol tsakanin Fabrairu da Mayun 2023, ban da wasu zarge-zargen rashawa da ake yi mata.
“Mutanen Kano har yanzu ba su manta da bidiyon dala na tsohon gwamna kuma shugaban riƙon jam’iyyar APC ba,” in ji sanarwar.
Gwamnatin ta yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su kiyaye ka’idojin aikin jarida su guji zama masu ruɗar da jama’a.
Ta ce ba ta da abin ɓoyewa, kuma jami’anta a shirye suke su amsa tambayoyin hukumomin yaƙi da cin hanci duk lokacin da ake buƙata.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Wannan zargi ƙarya ne da ’yan adawa suka kitsa a matsayin farfaganda domin neman suna a siyasance.”
Ta jaddada cewa gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da hankali kan mulkin nagari, tattalin dukiyar jama’a da inganta rayuwar al’umma, tare da gargaɗin ’yan adawa da cewa idan suka ci gaba da yaɗa bayanan ƙarya, za a ɗauki matakin shari’a a kansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abdullahi Ibrahim Rogo Sanusi Bature Dawakin Tofa Sanarwar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
A wani bidiyo daban da PUNCH Metro ta gani a Facebook, wanda Mc Pee ya wallafa, wani mutum da ake zargin dalibi ne na jami’ar ya bayyana abin da ya faru.
A cewarsa, marigayin ya roki a bar shi ya rayu kafin daga bisani wanda ake zargin ya kashe shi.
Ya ce: “Nanpon ya riga ya yanke Peter a kumatunsa yayin da yake rokon a bar shi. Lokacin da muka shiga tsakani muka ce ya daina, sai ya yi barazanar yanka duk wanda ya kusanto shi.
“Da Peter ya ga ba ya sauraron rokonsa, sai ya rungume shi yana rokonsa da kuka.
“Mun fita neman taimako amma babu wanda ya amsa mana. Da Peter ya yi kokarin tserewa sai ya fadi, Nanpon ya kamo shi ya ci gaba da saransa da adda.”
Wani kwararren masanin tsaro da yaki da ta’addanci ya wallafa a dandalin D a ranar Lahadi cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Jihar Filato sun kama wanda ake zargin.
Ya kuma ambaci majiyoyi da suka tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaro na jami’ar.
Ya rubuta cewa, “Rundunar ‘Yansanda ta Filato ta kama wani dalibi mai shekaru 23 na Jami’ar Jos bisa zargin kashe abokinsa sannan ya binne shi a rami mara zurfi a cikin dakinsa da ke kauyen Rusau a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.
“Majiyoyi sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi a Jos, inda suka danganta da rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaron jami’ar.
“A cewar majiyoyin, wanda ake zargin mai suna Dabid Nanpon Timmap, dalibi a matakin shekara ta uku a jami’ar, ya kai wa Peter Mata Mafurai, mai shekaru 22, hari da adda, ya kashe shi a gidansa.”
Zagazola ya kara da cewa, bayan samun kiran gaggawa da misalin karfe 9:30 na safiya, DPO na sashin Laranto ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa wurin, inda aka kama wanda ake zargin.
“Majiyoyin sun ce bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya binne mamacin a cikin rami mara zurfi da ya haka a cikin dakinsa. An tono gawar kuma an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham domin yin binciken gawar (autopsy),” in ji shi.
Ya kara da cewa, an tsare wanda ake zargin yayin da ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin dalilin kashe abokin nasa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA