Xi Jinping Ya Ziyarci Mambobin Majalisar CPPCC
Published: 6th, March 2025 GMT
Da yammacin yau Alhamis ne babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar, kana shugaban kwamitin kolin soja Xi Jinping, ya ziyarci mambobin taro na uku na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa wato CPPCC karo na 14 ta kasar Sin, wadanda suka zo daga kungiyar dimokuradiyya ta kasar Sin, da kungiyar raya dimokuradiyya ta kasar Sin, da kuma bangarorin ilimi.
Yayin ziyartar mambobin majalisar ta ba da shawara kan harkokin siyasa, Xi ya jadadda cewa, ya kamata a karfafa amfani da ilmi don inganta kimiyya da fasaha da kuma kwararru, ta yadda za a kafa wani yanayi na amfani da kwararru baki daya.
Bugu da kari, albarkacin bikin ranar mata ta kasa da kasa mai zuwa, a madadin kwamitin kolin JKS, Xi Jinping ya mika sakon gaisuwa da fatan alheri ga wakilai mata, da mambobi mata, da ma’aikata mata da suka halarci manyan taruka biyu, da mata na dukkan kabilu, da na dukkan sassan kasar, da ‘yan uwa mata na yankin musamman na Hong Kong, da na yankin musamman na Macao, da na yankin Taiwan, da kuma Sinawa mata dake rayuwa a kasashen waje. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: ta kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030
Majalisar Wakilai ta umarci Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Shirya Jarabawar Afrika ta Yamma (WAEC) da su dakatar da shirin fara amfani da tsarin jarabawa ta kwamfuta a jarabawar kammala sakandare ta shekarar 2026.
Umarnin ya biyo bayan amincewa da wani kudiri na gaggawa da Kelechi Wogu ya gabatar a zaman majalisar na ranar Alhamis.
Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a ZariyaKudirin na Wogu mai taken: “Bukatar Daukar Mataki Don Kaucewa Yawan Faduwa a Jarabawar Kwamfuta da WAEC ke Shirin Gudanarwa a 2026,” ya yi gargadin cewa gaggauta amfani da tsarin na iya haifar da yawan faduwa da kuma jefa dalibai cikin damuwa.
Wogu ya nuna damuwa kan yadda Ma’aikatar Ilimi ke da niyyar ci gaba da tsarin jarabawa ta kwamfuta duk da adawar da ke fitowa daga Ƙungiyar Malamai ta Ƙasa da shugabannin makarantu, musamman a yankunan karkara inda fiye da kaso 70 cikin 100 na masu jarabawar ke zaune.
Ya ce yawancin makarantu, musamman a yankunan karkara, ba su da dakunan kwamfuta masu aiki, babu intanet, babu wutar ingantacciyar lantarki, kuma ba su da malamai masu ƙwarewa a fannin fasahar zamani.
Ya jaddada cewa fara amfani da tsarin a irin wannan yanayi zai zo da matsala, yana ambato matsalolin fasaha da suka shafi shafin sakamakon WAEC na 2025 a matsayin shaidar rashin shiri.
Domin magance waɗannan ƙalubale, Majalisar ta umarci Ma’aikatar Ilimi da ta haɗa kai da gwamnatocin jihohi domin saka ayyukan daukar malamai masu koyar da kwamfuta, gina dakunanta, samar da kayan intanet da kuma wutar lantarki a cikin kasafin kuɗin shekarar 2026 zuwa 2029.
Majalisar ta kuma yanke shawarar cewa kada a fara amfani da tsarin jarabawar kafin shekarar karatu ta 2030.
Majalisar ta amince da kudirin gaba ɗaya, tare da umartar kwamitocinta kan Ilimi a matakin farko, Fasahar Zamani da Bayani, Hukumomin Jarabawa, da Ma’aikata da su tattauna da masu ruwa da tsaki sannan su gabatar da rahoto cikin makonni huɗu domin ɗaukar matakin dokoki na gaba.
An kirkiro da tsarin jarabawa da kwamfuta ne a Najeriya ne domin rage yawan magudin jarabawa da kuma sabunta tsarin ilimi na ƙasa.