Aminiya:
2025-09-17@21:52:12 GMT

Gwamnatin Kano ta ayyana hutu gobe Juma’a

Published: 11th, September 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta ayyana gobe Juma’a, 12 ga watan Satumban 2025, wadda za ta yi daidai da 19 ga watan Rabi’ul Awwal na 1447, a matsayin ranar hutun Takutaha.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Sakataren Ofishin Shugaban Ma’aikatan Jihar, Salisu Mustapha, ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta bayyana cewa hutun yana cikin girmama ranar bakwai ga haihuwar Annabi Muhammad (S.

A.W).

Daruruwan magoya bayan NNPP sun tarbi Kwankwaso a Kalaba Kotu ta yanke wa jagoran Ansaru hukuncin ɗaurin shekaru 15

“Mutanen Kano sun shafe shekaru suna bikin wannan rana a matsayin Ranar Takutaha.

“Bikin Ranar Takutaha wani tsohon tarihi ne da aka shafe shekaru aru-aru ana gudanarwa.”

Gwamnan ya buƙaci al’ummar jihar da su yi amfani da wannan lokacin domin yin tuntuntuni a kan koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da sanya su cikin harkokinsu na yau da kullum.

Ya kuma buƙaci jama’a da su riƙa yin addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaba a Kano da Nijeriya baki ɗaya.

Ya yi addu’ar Allah Ya shiga al’amuranmu a wannan lokaci mawuyaci, Ya kuma ba mu albarkacin wannan damuna.

Idan ba a manta ba, Gwamnatin Tarayya ta ayyana Juma’ar makon jiya a matsayin ranar hutun Maulidi, domin bai wa Musulmi damar murnar zagayowar ranar haihuwar Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (S.A.W).

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Watan Maulidi

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata