Yadda zanga-zangar adawa da rashawa ta rikiɗe zuwa tarzoma a Nepal
Published: 10th, September 2025 GMT
Rabi Laxmi Chitrakar, matar tsohon Firaministan Nepal, Jhalanath Khanal, ta rasu bayan masu zanga-zanga sun banka wa gidansu wuta a unguwar Dallu da ke birnin Kathmandu a ranar Talata.
Bayanai sun ce masu zanga-zanga a ƙasar mai tsaunuka da ke fama da tashin hankali mafi muni cikin shekaru da dama sun tarfa matar tsohon firaministan ne a cikin gida kafin su kunna wutar.
An garzaya da ita asibitin kula da waɗanda ibtila’in ƙuna ya afkawa da ke Kirtipur cikin mummunan yanayi, amma daga ƙarshe ta ce ga garinku nan sakamakon munanan raunuka da ta samu.
Rasuwarta ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da zanga-zangar matasa a duk faɗin Nepal tsawon kwana biyu, duk da cewa gwamnati ta ɗage takunkumin da ta saka kan kafafen sada zumunta a farkon makon nan.
Masu zanga-zangar na neman jami’an gwamnati sauka daga kujeru saboda zargin cin hanci da rashawa, nuna son kai a siyasa da kuma taɓaɓarewar tattalin arziki.
Tun dai daga ranar Litinin aka fara tashin hankali, kuma rahotanni sun nuna cewa aƙalla mutum 22 sun mutu yayin da sama da 300 suka ji rauni.
Kungiyar Amnesty International ta zargi ’yan sanda da amfani da harsasai wajen tarwatsa masu zanga-zangar.
Bidiyoyin da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna yadda ake jefa bama-bamai da aka haɗa da man fetur a gidajen fitattun ’yan siyasa, ciki har da na tsofaffin Firaministoci — K.P. Sharma Oli, Sher Bahadur Deuba, da kuma Pushpa Kamal Dahal.
Muhimman gine-ginen gwamnati, ciki har da Singha Durbar (hedikwatar gwamnati) da fadar shugaban ƙasa, Sheetal Niwas, su ma an kai musu hari.
A yayin da tashin hankali ke ƙara tsananta ne Firaminista K.P Sharma Oli mai shekaru 73, ya miƙa takardar murabus ga shugaban ƙasa a ranar Talata, yana mai cewa matakin “na da muhimmanci don ɗaukar matakan samun mafita a siyasar ƙasar.”
Haka kuma, wasu ministocin gwamnati da suka haɗa da na ruwa, noma da cikin gida, sun yi murabus, domin nuna adawa da yadda tarzomar ke ƙara tsananta.
Yanzu haka dai ƙasar ta faɗa cikin wani yanayi na fargaba a yayin da hukumomi ke ƙoƙarin dawo da doka da oda, inda ake ta kira da a koma kan teburin tattaunawa domin kawo ƙarshen rikicin.
A yayin da sojoji suka ayyana dokar hana fita tare da gudanar da sintiri a birnin Kathmandu, matasan Nepal da suka gudanar da zanga-zangar da sunan adawa da cin hanci da rashawa sun yi iƙirarin cewa wasu masu neman dama ne suka ƙwace zanga-zangar wadda ta rikiɗe ta zuwa tashin hankali.
Ƙungiyoyin matasa sun nesanta kansu daga ɓarnar, suna masu cewa masu son yin amfani da dama ne suka shiga suka lalata zanga-zangar.
Sojojin da suka kafa dokar hana fita a faɗin ƙasa har zuwa safiyar Alhamis, sun yi gargaɗin hukunta duk wanda aka samu da hannu a tashin hankali ko ɓarna.
Rahotanni sun ce an kama mutum 27 da ake zargi da hannu a fashi da tarzoma, tare da ƙwato bindigogi 31.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rabi Laxmi Chitrakar zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.
A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp