Aminiya:
2025-11-02@17:03:40 GMT

Yadda zanga-zangar adawa da rashawa ta rikiɗe zuwa tarzoma a Nepal

Published: 10th, September 2025 GMT

Rabi Laxmi Chitrakar, matar tsohon Firaministan Nepal, Jhalanath Khanal, ta rasu bayan masu zanga-zanga sun banka wa gidansu wuta a unguwar Dallu da ke birnin Kathmandu a ranar Talata.

Bayanai sun ce masu zanga-zanga a ƙasar mai tsaunuka da ke fama da tashin hankali mafi muni cikin shekaru da dama sun tarfa matar tsohon firaministan ne a cikin gida kafin su kunna wutar.

An harbe ’yan sanda 3 har lahira a Kogi An harbe ’yan sanda 3 har lahira a Kogi

An garzaya da ita asibitin kula da waɗanda ibtila’in ƙuna ya afkawa da ke Kirtipur cikin mummunan yanayi, amma daga ƙarshe ta ce ga garinku nan sakamakon munanan raunuka da ta samu.

Rasuwarta ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da zanga-zangar matasa a duk faɗin Nepal tsawon kwana biyu, duk da cewa gwamnati ta ɗage takunkumin da ta saka kan kafafen sada zumunta a farkon makon nan.

Masu zanga-zangar na neman jami’an gwamnati sauka daga kujeru saboda zargin cin hanci da rashawa, nuna son kai a siyasa da kuma taɓaɓarewar tattalin arziki.

Tun dai daga ranar Litinin aka fara tashin hankali, kuma rahotanni sun nuna cewa aƙalla mutum 22 sun mutu yayin da sama da 300 suka ji rauni.

Kungiyar Amnesty International ta zargi ’yan sanda da amfani da harsasai wajen tarwatsa masu zanga-zangar.

Bidiyoyin da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna yadda ake jefa bama-bamai da aka haɗa da man fetur a gidajen fitattun ’yan siyasa, ciki har da na tsofaffin Firaministoci — K.P. Sharma Oli, Sher Bahadur Deuba, da kuma Pushpa Kamal Dahal.

Muhimman gine-ginen gwamnati, ciki har da Singha Durbar (hedikwatar gwamnati) da fadar shugaban ƙasa, Sheetal Niwas, su ma an kai musu hari.

A yayin da tashin hankali ke ƙara tsananta ne Firaminista K.P Sharma Oli mai shekaru 73, ya miƙa takardar murabus ga shugaban ƙasa a ranar Talata, yana mai cewa matakin “na da muhimmanci don ɗaukar matakan samun mafita a siyasar ƙasar.”

Haka kuma, wasu ministocin gwamnati da suka haɗa da na ruwa, noma da cikin gida, sun yi murabus, domin nuna adawa da yadda tarzomar ke ƙara tsananta.

Yanzu haka dai ƙasar ta faɗa cikin wani yanayi na fargaba a yayin da hukumomi ke ƙoƙarin dawo da doka da oda, inda ake ta kira da a koma kan teburin tattaunawa domin kawo ƙarshen rikicin.

A yayin da sojoji suka ayyana dokar hana fita tare da gudanar da sintiri a birnin Kathmandu, matasan Nepal da suka gudanar da zanga-zangar da sunan adawa da cin hanci da rashawa sun yi iƙirarin cewa wasu masu neman dama ne suka ƙwace zanga-zangar wadda ta rikiɗe ta zuwa tashin hankali.

Ƙungiyoyin matasa sun nesanta kansu daga ɓarnar, suna masu cewa masu son yin amfani da dama ne suka shiga suka lalata zanga-zangar.

Sojojin da suka kafa dokar hana fita a faɗin ƙasa har zuwa safiyar Alhamis, sun yi gargaɗin hukunta duk wanda aka samu da hannu a tashin hankali ko ɓarna.

Rahotanni sun ce an kama mutum 27 da ake zargi da hannu a fashi da tarzoma, tare da ƙwato bindigogi 31.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rabi Laxmi Chitrakar zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.

Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.

Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.

A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.

“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025 Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum