Aminiya:
2025-09-17@21:51:38 GMT

Ganawa da Tinubu: Buƙatun Gwamnonin Arewa maso Gabas

Published: 4th, September 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya jagoranci tawagar gwamnonin Arewa maso Gabas zuwa fadar shugaban ƙasa domin ganawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ranar Laraba.

Ganawar  wanda aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, ta mayar da hankali ne kan muhimman batutuwan da suka shafi yankin Arewa maso Gabas da suka haɗa da kammala muhimman ayyukan gina hanyoyin mota 17 cikin gaggawa, da kuma ci gaba da haƙo mai a rijiyoyin kan iyaka, musamman ma rijiyoyin Kolmani da tafkin Chadi.

Matasa sun kashe ’yan bindiga 6 sun sha alwashin kare kansu Mai taɓin hankali ta haihu a tsakiyar kasuwa a Oyo

Sauran gwamnonin da suka halarci ganawar sun haɗa da: Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad da Gwamnan Ypbe, Mai Mala Buni da Gwamnan Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri da kuma Gwamnan Taraba Agbu Keffas.

Da yake gabatar da jawabinsa a yayin taron ganawar, Gwamnan Zulum wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa maso Gabas, ya buƙaci shugaban ƙasar da ya kammala ayyukan tituna da kuma gina muhimman hanyoyin da suka haɗa jihohi shida na shiyyar.

Hanyoyin sun haɗa da: Titin Kano zuwa Maiduguri, titin jirgin ƙasa na Fatakwal-Jos zuwa Bauchi zuwa Maiduguri, da titin Bama zuwa Mubi zuwa Yola, da titin Wukari zuwa Jalingo zuwa Yola, da titin Duguri zuwa Mansur (NNPC project, titin Bauchi zuwa Gombe zuwa Biu zuwa Damaturu da titin Damaturu zuwa Geidam da  titin Gombe zuwa Poli-Geidam, titin Gombe-Poli-Ningi da titin Bauchi zuwa Ningi da titin Bauchi-Ningi sai Damaturu-Biu.

Sauran sun haɗa da titin Alkaleri zuwa Futuk da titin Maiduguri zuwa Damboa zuwa Yola, da titin Gombe-Dukku-Darazo da titin Biu-Gombe da titin Ibi-Shamdam, titin Maiduguri zuwa Monguno-Baga da titin Maiduguri-Ngala zuwa Bama-Banki.

Gwamna Zulum ya yaba wa shugaban ƙasa, bisa jajircewar da yake yi na ƙoƙarin maido da zaman lafiya a yankin Arewa maso gabas, inda ya ce, “Mun gode maka da ka samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da kuma ci gaba da yunƙurin ganin an ci gaba da yaƙi da ’yan tada ƙayar baya.

Ya kuma tabbatar wa shugaban ƙasar kan ƙudirinsu na ganin gwamnatinsa ta samar da horo na musamman ga ma’aikata don samar da fasahar ƙere-ƙere da nufin magance matsalar rashin tsaro da yankin Arewa maso Gabas ke fuskanta.

“Muna da cikakkiyar daidaituwa tare da kyakkyawan shiri na shugaban ƙasa na horar da ma’aikata da kuma samar da fasaha da nufin kawar da mummunan halin da ake ciki a cikin dazuzzuka, ta yadda za a rage ta’addanci da kuma inganta ci gaban noma tare da sabunta ajandar samar da abinci,” in ji Zulum.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara

Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.

Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.

“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.

Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.

Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago