Ganawa da Tinubu: Buƙatun Gwamnonin Arewa maso Gabas
Published: 4th, September 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya jagoranci tawagar gwamnonin Arewa maso Gabas zuwa fadar shugaban ƙasa domin ganawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ranar Laraba.
Ganawar wanda aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, ta mayar da hankali ne kan muhimman batutuwan da suka shafi yankin Arewa maso Gabas da suka haɗa da kammala muhimman ayyukan gina hanyoyin mota 17 cikin gaggawa, da kuma ci gaba da haƙo mai a rijiyoyin kan iyaka, musamman ma rijiyoyin Kolmani da tafkin Chadi.
Sauran gwamnonin da suka halarci ganawar sun haɗa da: Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad da Gwamnan Ypbe, Mai Mala Buni da Gwamnan Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri da kuma Gwamnan Taraba Agbu Keffas.
Da yake gabatar da jawabinsa a yayin taron ganawar, Gwamnan Zulum wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa maso Gabas, ya buƙaci shugaban ƙasar da ya kammala ayyukan tituna da kuma gina muhimman hanyoyin da suka haɗa jihohi shida na shiyyar.
Hanyoyin sun haɗa da: Titin Kano zuwa Maiduguri, titin jirgin ƙasa na Fatakwal-Jos zuwa Bauchi zuwa Maiduguri, da titin Bama zuwa Mubi zuwa Yola, da titin Wukari zuwa Jalingo zuwa Yola, da titin Duguri zuwa Mansur (NNPC project, titin Bauchi zuwa Gombe zuwa Biu zuwa Damaturu da titin Damaturu zuwa Geidam da titin Gombe zuwa Poli-Geidam, titin Gombe-Poli-Ningi da titin Bauchi zuwa Ningi da titin Bauchi-Ningi sai Damaturu-Biu.
Sauran sun haɗa da titin Alkaleri zuwa Futuk da titin Maiduguri zuwa Damboa zuwa Yola, da titin Gombe-Dukku-Darazo da titin Biu-Gombe da titin Ibi-Shamdam, titin Maiduguri zuwa Monguno-Baga da titin Maiduguri-Ngala zuwa Bama-Banki.
Gwamna Zulum ya yaba wa shugaban ƙasa, bisa jajircewar da yake yi na ƙoƙarin maido da zaman lafiya a yankin Arewa maso gabas, inda ya ce, “Mun gode maka da ka samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da kuma ci gaba da yunƙurin ganin an ci gaba da yaƙi da ’yan tada ƙayar baya.
Ya kuma tabbatar wa shugaban ƙasar kan ƙudirinsu na ganin gwamnatinsa ta samar da horo na musamman ga ma’aikata don samar da fasahar ƙere-ƙere da nufin magance matsalar rashin tsaro da yankin Arewa maso Gabas ke fuskanta.
“Muna da cikakkiyar daidaituwa tare da kyakkyawan shiri na shugaban ƙasa na horar da ma’aikata da kuma samar da fasaha da nufin kawar da mummunan halin da ake ciki a cikin dazuzzuka, ta yadda za a rage ta’addanci da kuma inganta ci gaban noma tare da sabunta ajandar samar da abinci,” in ji Zulum.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkukuMai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.
Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.
Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.
Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.
Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.
Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.
Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.
“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,” in ji alkalin.
Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.
Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.
Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.