Aminiya:
2025-11-02@06:38:18 GMT

2027: ’Yan adawa na ƙoƙarin sanya APC fara kamfe da wuri — Tinubu

Published: 4th, September 2025 GMT

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya zargi jam’iyyun adawa da jan APC cikin harkokin siyasa kafin lokacin zaɓen 2027.

Sai dai ya ce ba zai bari hakan ya karkatar da hankalinsa daga shugabantar Najeriya ba.

NAJERIYA A YAU: Hare-hare Kan Tarurrukan Siyasa Da Alakarsu da 2027 Za a koma rubuta jarabawar WAEC a komfuta

Yayin da yake ganawa da gwamnonin Arewa maso Gabas a Abuja, Tinubu ya yaba da ƙoƙrinsu wajen yaƙi da rashin tsaro tare da alƙawarin yin aiki da su kan batun ’yan sandan jihohi da kuma ayyukan gina hanyoyi.

“A siyasa, ’yan adawa suna ƙoƙarin janyo mu mu fara kamfen da wuri. Amma duk da haka, ba zan bari a karkatar da hankalina ba. Na mayar da hankali ne kan abin da ke gabana,” in ji Tinubu.

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, wanda ya yi magana a madadin sauran gwamnonin, ya tabbatar wa shugaban ƙasa da goyon bayansu.

Ya bayyana matsalolin tsaro a Arewa maso Gabas tare da roƙon ƙarin tallafin Gwamnatin Tarayya.

“Muna goyon bayan shirin shugaban ƙasa na horas da ma’aikata da kuma samar da fasaha domin rage matsalar ta’addanci da inganta harkar noma,” in ji Zulum.

Gwamnonin sun kuma roƙi shugaban ƙasa ya kammala manyan hanyoyi, ya ci gaba da aikin haƙo mai a Kolmani da Tafkin Chadi, da kuma ci gaba da ayyukan soji a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas Gwamnoni Shugabab Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’

Jami’an diflomasiyya a Tanzania sun ce akwai kwararan hujjoji da ke tabbatar da an kashe akalla mutum 500 a cikin kwana biyu da barkewar zanga-zangar kin amincewa da sakamakon zaben da aka gudanar a ranar Laraba.

Sai dai a wani bangaren kuma, alkalumman Yan’adawa sun zarta haka.

Wakiliyar BBC ta ce ministan harakokin wajen Tanzania Mahmoud Kombo Thabit ya musanta rahotannin, amma wani jagoran adawa John Kitoka ya ce ‘yansanda da wasu sojojin haya na kasashen waje ne suka aiwatar da kisan mutane cikin dare.

Majalisar Dinkin Dauniya ta yi kiran gudanar da bincike kan zargin amfani da karfin da ya wuce kima a kan masu zanga-zangar.

 

BBC

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
  • Tinubu ya ƙirƙiri sabon harajin da zai iya ƙara N100 a kan kowacce litar man fetur