Aminiya:
2025-11-02@12:30:11 GMT

Mai taɓin hankali ta haihu a tsakiyar kasuwa a Oyo

Published: 4th, September 2025 GMT

Wata mata mai tabin hankali da ba a iya gano danginta ba, ta haihu a bainar jama’a a cikin kasuwar garin Aarinoye a karamar hukumar Itesiwaju ta Jihar Oyo.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa matar ta haihu ne da misalin karfe 5:00;na yammacin ranar Laraba, kuma ta haifi jaririnta namiji lami lafiya ba tare da tallafin unguwar-zoma ba.

‘Za a tafka mamakon ruwan saman da zai iya haifar da ambaliya a jihohi 14’ Duk budurwar da ta ci kuɗin saurayi kuma ta ƙi zuwa wajensa ta karya doka – ’Yan sanda

Majiyar ta ce kafin matar ta haihu an saba ganinta daga safiya zuwa daren kowace rana dauke da juna biyu tana yawon tsintar dagwalon abinci da shan gurɓataccen ruwa a cikin bola.

idan dare ya yi kuma, majiyar ta ce matar takan koma bayan ginin gidan rediyo na BCOS na Oke Ogun, inda take kwana a kasa ba tare da shimfida ko mayafi ba.

Jim kaɗan bayan haihuwar, mazauna yankin sun hanzarta daukar matakin karbar jaririn daga hannun wannan mata sannan suka mika shi ga babban Jami’in ‘yan sanda (DPO) na yankin.

A nan take ne jami’in ya nemi wasu mata da suka taimaka wajen tsaftace jikin mai jegon da jaririn nata kamar yadda ake yi wa mata masu jego, sannan aka garzaya da ita zuwa wani asibiti a garin Otu hedkwatar karamar hukumar Itesiwaju domin kula da lafiyarta.

Rundunar ’Yan sanda a Jihar ta Oyo ta nemi al’ummar wannan yanki na Aarinoye da su taimaka da ingantaccen bayanin da zai kai ga gano dangi ko mijin wannan matar mai tabin hankali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haihuwa Mai rabin hankali

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata