Aminiya:
2025-09-17@21:51:02 GMT

’Yan bindiga sun sace basarake a Kogi

Published: 3rd, September 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Hakimin Bagaji Odo a Karamar Hukumar Omala ta Jihar Kogi, David Wada.

Rahotanni sun ce basaraken ya faɗa tarkon ’yan bindigar ne a ƙauyen Ojuwo Ugweche da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Litinin, yayin da yake dawowa daga taron sarakunan gargajiya a Abejukolo, hedikwatar ƙaramar hukumar.

’Yan sanda sun kama ɗan bindiga da shanu 10 a Kebbi Gwamnatin Kano za ta sake yi wa zawarawa da ’yan mata auren gata

Wani mazaunin yankin, Maji Ahiaba, ya bayyana cewa a ’yan kwanakin nan ƙauyen Ojuwo Ugweche na fuskantar hare-haren masu ta’adar garkuwa da mutane, duk da cewa a baya an taɓa tura jami’an tsaro da ’yan sa-kai domin daƙile ayyukan miyagun.

Sai dai a cewar mazaunin a wannan karo da abun ya faru, babu jami’in tsaro ko guda a yankin.

Shugaban majalisar sarakunan gargajiya na ƙaramar hukumar, Sarkin Ife, Mai Martaba Boniface Musa, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya roƙi jami’an tsaro su bi sahun masu garkuwar domin ceto basaraken da aka sace.

Kakakin rundunar ’yan sanda ta Jihar Kogi, SP Williams Aya, ya ce tuni an tura jami’an tsaro, mafarauta da kuma ’yan sa-kai domin su tsefe dajin da ake zargin an kai sarkin da zummar ceto shi cikin aminci.

Sai dai har yanzu iyalai da kuma al’ummar yankin na cikin fargaba, la’akari da cewa tun bayan sace basaraken babu wanda masu garkuwar suka tuntuɓa.

A bara ne wani rikicin ƙabilanci da ya ɓarke a Bagana, Bagaji, Agojeju Odo da Ajokpachi Odo ya bai wa ’yan bindiga damar kashe ɗaruruwan mutane a yankin, lamarin da aka samu aminci bayan Gwamna Usman Ahmed Odo ya tura sojoji da jami’an tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kogi jami an tsaro yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na kira ga Amurka, da ta gaggauta dakatar da shuka kiyayya, da haifar da tashin hankali, da rura wutar gaba a tekun kudancin kasar Sin, kana ta kyale a dawo da yanayin zaman lafiya da daidaito a yankin. Lin Jian, ya bayyana hakan ne yau Litinin, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, lokacin da aka yi masa tambaya kan batun.

Wasu rahotanni daga kafofin watsa labarai sun bayyana cewa, a baya bayan nan, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ya fitar da sanarwa dake cewa Amurka na goyon bayan kasar Philippines, game da watsi da ta yi da tsare-tsaren kasar Sin na kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin Huangyan Dao.

Lin ya ce “Mun gabatar da kakkarfan korafi a yau, dangane da kuskuren da Amurka ta tafka. Tsibirin Huangyan Dao yankin kasar Sin ne tun fil azal”, kuma kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin na karkashin ikon mulkin kai na Sin, wanda hakan ke nufin yana bisa turba, ya dace da doka, bai kuma cancanci suka ba. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin