’Yan bindiga sun sace basarake a Kogi
Published: 3rd, September 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Hakimin Bagaji Odo a Karamar Hukumar Omala ta Jihar Kogi, David Wada.
Rahotanni sun ce basaraken ya faɗa tarkon ’yan bindigar ne a ƙauyen Ojuwo Ugweche da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Litinin, yayin da yake dawowa daga taron sarakunan gargajiya a Abejukolo, hedikwatar ƙaramar hukumar.
Wani mazaunin yankin, Maji Ahiaba, ya bayyana cewa a ’yan kwanakin nan ƙauyen Ojuwo Ugweche na fuskantar hare-haren masu ta’adar garkuwa da mutane, duk da cewa a baya an taɓa tura jami’an tsaro da ’yan sa-kai domin daƙile ayyukan miyagun.
Sai dai a cewar mazaunin a wannan karo da abun ya faru, babu jami’in tsaro ko guda a yankin.
Shugaban majalisar sarakunan gargajiya na ƙaramar hukumar, Sarkin Ife, Mai Martaba Boniface Musa, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya roƙi jami’an tsaro su bi sahun masu garkuwar domin ceto basaraken da aka sace.
Kakakin rundunar ’yan sanda ta Jihar Kogi, SP Williams Aya, ya ce tuni an tura jami’an tsaro, mafarauta da kuma ’yan sa-kai domin su tsefe dajin da ake zargin an kai sarkin da zummar ceto shi cikin aminci.
Sai dai har yanzu iyalai da kuma al’ummar yankin na cikin fargaba, la’akari da cewa tun bayan sace basaraken babu wanda masu garkuwar suka tuntuɓa.
A bara ne wani rikicin ƙabilanci da ya ɓarke a Bagana, Bagaji, Agojeju Odo da Ajokpachi Odo ya bai wa ’yan bindiga damar kashe ɗaruruwan mutane a yankin, lamarin da aka samu aminci bayan Gwamna Usman Ahmed Odo ya tura sojoji da jami’an tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kogi jami an tsaro yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta raba zunzurutun kuɗi naira miliyan 63.4 ga iyalan jami’anta 84 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.
Rundunar ta raba kudin ne a ƙarƙashin tsarin inshorar rayuwa da kuma tsarin kula da lafiyar iyali na Sufeto Janar na ’yan sanda.
An gudanar da rabon kuɗin ne a ranar Alhamis a Maiduguri babban birnin jihar kamar yadda Kakakin rundunar a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana a cikin wata sanarwa.
A cewar sanarwar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, wanda ya wakilci Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun, shi ne ya gabatar da takardun cakin kudin ga iyalan waɗanda suka ci gajiyar tallafin.
“Harkokin da suka shafi jami’anmu da iyalansu ya kasance babban fifiko ga rundunar,” in ji CP Abdulmajid yayin taron.
Ya ce wannan shiri na nuna tausayi da rikon amana, da kuma jagoranci mai nagarta daga Sufeto Janar wajen girmama jaruman da suka sadaukar da rayukansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron ƙasa.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyalan da suka amfana da tallafin da su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace, musamman wajen tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, da jin daɗin rayuwar iyalansu gaba ɗaya.
Ya yaba wa Sufeto Janar bisa ci gaba da tsare-tsaren jin daɗin jami’an rundunar, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyin da ke samar da agaji da kwanciyar hankali ga iyalan waɗanda suka rasa masoyansu.
A nata jawabin a madadin iyalan da suka amfana, Misis Nana Goni ta nuna godiya ga Sufeto Janar bisa goyon bayan da ya bayar, tana mai tabbatar da cewa za su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya kamata don inganta rayuwar iyalansu.
Rundunar ta bayyana cewa wannan rabon tallafi ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kula da walwala da mutuncin jami’anta da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma.