Aminiya:
2025-11-02@12:30:17 GMT

Kilishiyar Waja ta tallafa wa matan gidan yari da kayayyaki a Gombe

Published: 31st, August 2025 GMT

Kilishiyar Waja, Hajiya Rabee Abubakar Kulani, ta kai ziyara gidan gyaran hali na Gombe, inda ta raba mata fursunoni kayan tsaftar jiki domin su kula da kansu a lokacin al’ada.

Ta ce ta kai wannan gudummawa ne domin tallafa wa mata fursunoni wajen kare mutuncinsu, ganin cewa sau da yawa ba su da damar samun irin waɗannan muhimman kayayyaki.

Gwamnatin Sakkwato za ta fara biyan masallatan Juma’a kuɗi duk wata Zaɓen Ribas: APC ta yi nasara a ƙananan hukumomi 20, PDP ta samu 3

“Ina so su ji kamar sauran mata, su samu tsafta da mutunci duk da yanayin da suke ciki.

“Shi ya sa na sayi kayayyakin da kaina domin na tallafa musu,” in ji ta.

A yayin ziyarar, ta kuma tattauna da su kan batun lafiya da haƙƙin haihuwa, tare da jaddada muhimmancin tsaftar al’ada.

Ta samu rakiyar Hajiya Hauwa Saraki, shugabar NCWS a Gombe, da kuma Hauwa Musa Babaji, mai fafutukar kare haƙƙin mata.

Sun yaba da yadda aka samu ci gaba wajen kula da jin daɗin fursunoni idan aka kwatanta da shekarun baya.

Shugaban gidan gyaran hali na Gombe, DCC Victor Odafen, ya gode mata bisa wannan tallafi.

Ya kuma yi kira ga ƙungiyoyi da mutane masu hali su yi koyi da ita wajen tallafa wa fursunoni.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidan Yari Kilishiyar Waja

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

 

Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.

 

Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka October 31, 2025 Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata