Kilishiyar Waja ta tallafa wa matan gidan yari da kayayyaki a Gombe
Published: 31st, August 2025 GMT
Kilishiyar Waja, Hajiya Rabee Abubakar Kulani, ta kai ziyara gidan gyaran hali na Gombe, inda ta raba mata fursunoni kayan tsaftar jiki domin su kula da kansu a lokacin al’ada.
Ta ce ta kai wannan gudummawa ne domin tallafa wa mata fursunoni wajen kare mutuncinsu, ganin cewa sau da yawa ba su da damar samun irin waɗannan muhimman kayayyaki.
“Ina so su ji kamar sauran mata, su samu tsafta da mutunci duk da yanayin da suke ciki.
“Shi ya sa na sayi kayayyakin da kaina domin na tallafa musu,” in ji ta.
A yayin ziyarar, ta kuma tattauna da su kan batun lafiya da haƙƙin haihuwa, tare da jaddada muhimmancin tsaftar al’ada.
Ta samu rakiyar Hajiya Hauwa Saraki, shugabar NCWS a Gombe, da kuma Hauwa Musa Babaji, mai fafutukar kare haƙƙin mata.
Sun yaba da yadda aka samu ci gaba wajen kula da jin daɗin fursunoni idan aka kwatanta da shekarun baya.
Shugaban gidan gyaran hali na Gombe, DCC Victor Odafen, ya gode mata bisa wannan tallafi.
Ya kuma yi kira ga ƙungiyoyi da mutane masu hali su yi koyi da ita wajen tallafa wa fursunoni.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidan Yari Kilishiyar Waja
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.
Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA