Leadership News Hausa:
2025-11-02@03:37:28 GMT

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

Published: 31st, August 2025 GMT

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

Da ma can an yi ta ba da shawara cewa ya kamata Arsenal ta dauki danwasa mai buga gefen hagu kamar Gabriel Martinelli, amma ba ta ce komai ba har sai yanzu. Bayan da cinikin Eze ya fada, yanzu kuma kungiyar ta Arsenal ta sake mayar da hankalinta wajen sayan dan wasan baya daga kungiyar kwallon kafa ta Bayer Liberkusen, wato Piero Hincapie.

 

Chelsea

Da alama har yanzu mai horarwa Enzo Maresca bai hakura da karin cefane ba kafin rufe kasuwar, yayin da yake neman Alejandro Garnacho na Man United da danwasan RB Leipzig Dabi Simons. Sai dai komai zai dogara ne da yawan ‘yanwasan da ta iya sayarwa kamar Nicolas Jackson da Christopher Nkunku da Tyrikue George, wadanda duka kungiyar ta saka a kasuwa. Kociyan zai kuma so ya karfafa bayansa saboda yadda aka ce Lebi Colwill ba zai buga mafi yawan gasar bana ba saboda rauni a gwiwarsa.

 

Crystal Palace

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ba ta yi wata sayayyar kirki ba zuwa yanzu, amma ana sa ran abubuwa za su sauya nan gaba kadan saboda mai horarwa Oliber Glasner na neman danwasan gaba da na baya. Za a yi yunkurin ne saboda makomar ɗanbaya kuma kyaftin dinta Marc Guehi, wanda Liberpool da Manchester City suke zawarci sai kuma danwasan gaba Eberechi Eze, wanda tuni ya koma Arsenal. Ana ci gaba da alakanta Palace da Jeremy Jackuet na Rennes, yayin da kuma take harin danwasan tsakiya Bilal El Khannouss na Leicester City.

 

Liverpool

Mai koyar da ‘yan wasan Liberpool Arne Slot ya samu kudaden cefane masu yawa a bana wadanda ya sayi Florian Wirtz, da Jeremie Frimpong, da Milos Kerkez, da Hugo Ekitike, da Giobanni Leoni. Amma duk da haka yana fatan sake kashe miliyoyi wajen maye gurbin danwasan baya Jarell Kuansah da kuma sama wa Birgil ban Dijk abokin aiki. Ana sa ran za ta nemi Marc Guehi na Crystal Palace. Sai kuma turka-turkar sayen danwasan gaba Aledander Isak daga Newcastle, wanda har yanzu Liberpool bata fitar da ran za ta saya ba.

 

Manchester City

Manchester City ta sayi mafi yawan ‘yanwasanta tun kafin gasar Club World Cup, kuma wasu majiyoyi sun bayyana cewa ta gama sayayya. An yi ta rade-radin cewa tana son daukar mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain Gianluigi Donnarumma, amma tabbas wannan zai danganta ne da mai tsaron raga Ederson, wanda ake ganin shima zai iya barin kungiyar. Tottenham ta nuna sha’awar daukar Sabinho amma City ta ki amincewa zuwa yanzu. Amma idan ta yarda to hakan zai iya ba ta damar sayen danwasan Real Madrid Rodrygo.

 

Manchester United

Shima mai koyar da ‘yanwasan Manchester United Ruben Amorim ya mayar da hankalinsa kan bangaren gaba na tawagar tasa inda ya kashe fan miliyan 200 zuwa yanzu domin sayen Matheus Cunha, da Bryan Mbeumo, da Benjamin Sesko. Amma a bayyane take cewa United na da matsala a mai tsaron raga, yayin da Andre Onana ya gaza kuma shi ma Altay Bayindir ya fara aikata manyan kurakurai a wasansu da Arsenal. United na tunanin daukar Senne Lammens na Royal Antwarp.

 

Newcastle United

Har yanzu makomar Aledander Isak na cikin kokwanto duk da yunkurin mai horarwa Edie Howe na karfafa tawagarsa. Zuwa yanzu kungiyar ta sayi Anthony Elanga daga Bournemouth, da Jacob Ramsey daga Aston Billa, da Malick Thiaw daga AC Milan, kuma har yanzu kungiyar tana neman sayan dan wasan gaba kafin ta saki Aledandre Isak.

Yanzu dai kungiyar ta kwallafa kan Yoane Wissa amma kuma tana fuskantar turjiya daga Brentford saboda yadda ta ki yarda da tayin fan miliyan 40 kan dan wasan mai shekara 28 a duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kungiyar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Shugaba Bola Tinubu ya yi wa sabbin Shugabannin Sojoji ado da karin girma domin su dace da sabbin muƙamansu. Sabbin shugabannin rundunar sojin kasar da aka yi wa ado sun hada da Laftanar Janar, wanda yanzu ya zama Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS); da kuma Manjo Janar yanzu ya koma Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye Undiendeye a matsayin Babban Hafsan Tsaro na farin kaya (CDI). Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  Sauran su ne Manjo Janar, wanda yanzu ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Soja (COAS); Air Vice Marshal, wanda yanzu ya zama Air Marshal Kevin Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama; da kuma Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Vice Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa. Shugaba Tinubu ya sanar da maye gurbin Shugabannin Rundunar tsaron ne a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mataki da aka danganta da bukatar sake mai da hankali da kuma karfafa tsaron kasa. Bayan haka, Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin Shugabannin Rundunar tsaron da su dauki mataki mai tsauri kan barazanar tsaro da ke tasowa a fadin kasar, yana mai gargadin cewa ‘yan Nijeriya na tsammanin ganin sakamako, ba uzuri ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
  • Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC