An ƙone wata mata ƙurmus kan yi wa Annabi ɓatanci a Neja
Published: 31st, August 2025 GMT
Mazauna sun lakaɗa wa wata mata duka sannan suka ƙone ta ƙurmus kan zargin yi wa fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (SAW) ɓatanci a yankin Kasuwan-Garba da ke ƙaramar hukumar Mariga ta Jihar Neja.
Shaidu sun ce, lamarin ya faru ne a ranar Asabar lokacin da wata muhawara ta taso a cikin shagon matar inda take abincin sayarwa.
Aminiya ta ruwaito cewa, wani daga cikin kwastomomin matar ne cikin raha ya ce yana so ya aure ta domin ta zamo matarsa kamar yadda sunnar Ma’aiki (SAW) da tanadar, amma daga bisani lamarin ya haifar da cece-kuce har aka yi zargin ta furta kalaman ɓatanci.
Wani da ya buƙaci a sakaya sunansa ya ce an fara kai matar fadar Hakimin Kasuwan-Garba, inda daga nan aka miƙa ta hannun jami’an tsaro domin bincike.
Sai dai wasu gungun fusatattun matasa suka kwace matar mai suna Amaye daga hannun jami’an tsaron suka riƙa jifa da dukan da ya yi ajalinta.
Shugaban ƙaramar hukumar Mariga, Abbas Adamu Kasuwan-Garba, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa yanzu haka ƙura ta lafa kuma harkokin yau da kullum sun kankama.
Kazalika, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa “da misalin ƙarfe 2 na ranar 30 ga watan Agusta, an samu rahoto cewa wata mata mai suna Amaye ta yi wasu kalamai da aka ɗauka a matsayin ɓatanci ga Annabi (SAW).
“Wannan lamari ya jawo fushin jama’a da suka kai mata farmaki suka ƙone ta kafin isowar ƙarin jami’an tsaro.
“Yanzu haka ana ƙoƙarin cafke waɗanda suka aikata wannan aika-aika domin gudanar da bincike da gurfanar da su a kotu.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Neja
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.