Aminiya:
2025-11-02@06:26:23 GMT

Mutum 12 sun nutse bayan sake kifewar jirgin ruwa a Sakkwato

Published: 29th, August 2025 GMT

An sake samun damuwar kifewar jirgin ruwa a Ƙaramar hukumar Shagari inda jirgin ruwa ya nutse da mutane 12 a Ƙaramar hukumar ta Jihar Sakkwato wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu namiji da mace sauran 10 suka samu raununka.

Hatsarin ya faru ne da daren ranar Alhamis a gulbin Shagari inda mutane suka shiga cikin damuwa da kaɗuwa kan jirgin daya nutse da mutane da babur guda biyu da sauran kayan amfani, a wata ɗaya jirgi uku ya nutse a ruwa a Sakkwato.

Harbe soja: ’Yan sanda da Sojoji na binciken dalili a Bauchi Na bar APC saboda Tinubu bai cika alƙawarin da ya yi ba — Marafa

Nasir Umar wanda lamarin ya faru gaban idonsa ya ce, “jirgin ya nutse da mutane 12 da ya ɗauko daga garin Jaranja zuwa Ruggar Buda a mazaɓar Lambara,  kan hanyar ne ya kife a daren Alhamis  aka fitar inda mutum biyar sun samu rauni.

“Mutanen gari da suka kawo ɗauki ne suka taimaka kuma su ne suka ci gaba da aikin harranar Jumu’a, an yi nasarar fitar da mutum shida, biyar a raye ɗaya ya mutu, mace guda ta bata ba a ganta ba.

“Kan zurfin ruwan har yanzu ba a samu ceto mace daya da ta rage a ruwan ba, ana dai sa ran ba ta da rayuwa a yanzu,” a cewarsa.

Ya yi tir da halin da gwamnati ta nuna kan lamarin in da har aka ciro mutanen ba wani wakilin gwamnati da ke wurin, mutane ne suke taimakon junansu a gaban Sarkin Ruwa.

Kabir Lumu ya nuna kifewar jirgi da ake samu a kwanan nan sakaci ne na gwamnati domin ta ƙi samar da hanyoyin mota a wuraren da ruwa suka mamaye kuma sun ƙi samar da tsari mai kyau a harkar sufurin jiragen, sun ƙyale talakawa suna kowa tasa ta fishshe shi, matuƙar Gwamnatin Sakkwato ba ta dawo cikin hayyacinta ba kan wannan matsalar za a ci gaba da rasa mutane a jirgin ruwa.

A lokacin da yake tabbatar da faruwar lamarin mai bai wa gwamnan Sakkwato shawara kan Hukumar ba da agajin gaggawa ta jiha, Aminu Liman Bodinga ya ce sun tura jami’ansu inda lamarin ya faru don ba da taimakon da ake buƙata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakkwato Shagari jirgin ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.

Daga Abdullahi Shettima

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya wakilci Nijeriya a taron ƙoli na biranen Asiya da ya gudana a ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), inda ya gabatar da kudirorin sauyin ci gaban Kaduna.

Taron ya samu halartar manyan baki daga ƙasashe sama da 150, ciki har da gwamnoni, shugabannin birane da jagororin kasuwanci daga Asiya, Fasifik, Turai da Afirka. Taken taron shi ne “Haɗin Gwiwa. Ƙarfafawa. Sauyi.”

A jawabinsa mai taken “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa,” Gwamna Uba Sani ya bayyana yadda Kaduna ke samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma da tallafawa jama’a. Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki, kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su cim ma nasara a rayuwarsu.

Haka kuma, ya halarci baje kolin birnin Dubai mai taken “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira da Tasirin Zamantakewa,” inda ya jaddada muhimmancin jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha wajen buɗe damarmaki ga al’umma.

A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta-Janar na birnin Dubai, inda suka tattauna batutuwan kirkirar makamashin sharar gida, kula da sharar zamani, da tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.

Duk ɓangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin tattalin arzikin Kaduna zuwa mai ɗorewa.

Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun gaba wajen yin haɗin kai, ƙirƙira da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa — a Najeriya da duniya baki ɗaya.

Karshe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin