Mutum 12 sun nutse bayan sake kifewar jirgin ruwa a Sakkwato
Published: 29th, August 2025 GMT
An sake samun damuwar kifewar jirgin ruwa a Ƙaramar hukumar Shagari inda jirgin ruwa ya nutse da mutane 12 a Ƙaramar hukumar ta Jihar Sakkwato wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu namiji da mace sauran 10 suka samu raununka.
Hatsarin ya faru ne da daren ranar Alhamis a gulbin Shagari inda mutane suka shiga cikin damuwa da kaɗuwa kan jirgin daya nutse da mutane da babur guda biyu da sauran kayan amfani, a wata ɗaya jirgi uku ya nutse a ruwa a Sakkwato.
Nasir Umar wanda lamarin ya faru gaban idonsa ya ce, “jirgin ya nutse da mutane 12 da ya ɗauko daga garin Jaranja zuwa Ruggar Buda a mazaɓar Lambara, kan hanyar ne ya kife a daren Alhamis aka fitar inda mutum biyar sun samu rauni.
“Mutanen gari da suka kawo ɗauki ne suka taimaka kuma su ne suka ci gaba da aikin harranar Jumu’a, an yi nasarar fitar da mutum shida, biyar a raye ɗaya ya mutu, mace guda ta bata ba a ganta ba.
“Kan zurfin ruwan har yanzu ba a samu ceto mace daya da ta rage a ruwan ba, ana dai sa ran ba ta da rayuwa a yanzu,” a cewarsa.
Ya yi tir da halin da gwamnati ta nuna kan lamarin in da har aka ciro mutanen ba wani wakilin gwamnati da ke wurin, mutane ne suke taimakon junansu a gaban Sarkin Ruwa.
Kabir Lumu ya nuna kifewar jirgi da ake samu a kwanan nan sakaci ne na gwamnati domin ta ƙi samar da hanyoyin mota a wuraren da ruwa suka mamaye kuma sun ƙi samar da tsari mai kyau a harkar sufurin jiragen, sun ƙyale talakawa suna kowa tasa ta fishshe shi, matuƙar Gwamnatin Sakkwato ba ta dawo cikin hayyacinta ba kan wannan matsalar za a ci gaba da rasa mutane a jirgin ruwa.
A lokacin da yake tabbatar da faruwar lamarin mai bai wa gwamnan Sakkwato shawara kan Hukumar ba da agajin gaggawa ta jiha, Aminu Liman Bodinga ya ce sun tura jami’ansu inda lamarin ya faru don ba da taimakon da ake buƙata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sakkwato Shagari jirgin ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.
Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.
Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp