An fara gyaran layin dogon Abuja-Kaduna bayan hatsarin jirgin ƙasa
Published: 29th, August 2025 GMT
Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa ta Najeriya (NRC) ta fara aikin gyara layin dogon Abuja zuwa Kaduna da ya lalace sakamakon hatsarin jirgin kasa.
A ranar Talata da ta gabata ce jirgin mai tarago 10 da ya tashi da misalin karfe 11:00 na safe daga tasharsu da ke Kubwa a Abuja da nufin zuwa Kaduna, rikito daga kan hanyarsa a wata ƙaramar tasha da ke kauyen Asham, ’yan mintoci kalilan bayan fara tafiyar.
Injin jirgin da kuma tarago biyu da ke biye masa sun samu mummunar illa, a yayin da ragowar taragu shida suka goce daga kan layin, sai kuma guda da ke daukar manyan mutane.
Wakilinmu da ya koma tashar jirgin ta Kubwa a ranar Alhamis, ya samu labarin cewa hukumar ta NRC ta bayar da aikin gyaran ne ga wani kamfanin ƙasar Sin wanda kuma ya fara aikin gyaran a ranar Laraba da ta gabata.
An dai kai taragu ukun ne zuwa babban tashar hukumar da ke yankin Idu a Abuja, a yayin da a ke saran ɗauko ragowar shidan da kuma injin jirgin a ranar ta Alhamis, kamar yadda majiyar ta bayyana.
Bayanan sun ce ana sa ran a fara gyaran ɓangaren layin dogon a ranar ta Alhamis bayan an kawar da ragowan taragun shida da a cewar majiyar ba za su iya tafiya da kansu ba har sai an ɗaga su a sakamakon lalacewar da suka yi.
A wani labarin kuma, yawancin ma’aikata da ke aiki a tashar jirgin ƙasan ta Kubwa, da sauran masu gudanar da ayyuka a wajen na ci gaba da hutun dole, lamarin da ya mayar da wajen tamkar na yanayin zaman makoki.
Wasu daga cikin ma’aikata ’yan ƙalilan da su ka leƙa wurin aiki a ranar, sun shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya fi shafar ma’aikata da ke ɓangaren sayar da tikitin jirgi, da masu aikin tsaftace wajen, da masu yin dako, sai kuma direbobin tasi, da dai sauransu.
Ɗaya daga cikin ma’aikatan da aka zanta da shi ya koka a kan yadda lamarin inda ya ce ya raba su da sana’arsu da kuma jefa su a cikin halin kunci.
Wata da ke aiki da kamfanin samar da abincin maƙulashe da ke raba dafaffiyar taliyar ga fasinjoji kyauta a duk ranakun Alhamis da Juma’a da kuma Asabar, ta ce ta je wajen a ranan tare da cikakken fatan an fara aiki.
Jami’ar mai suna Joy Ene Agu ta ce suna raba taliyar ne kamar katan huɗu a kowane yini cikin ranakun a matsayin dabarun tallata taliyarsu ga jama’a, sannan su sayar da ɗanyarta ga masu sha’awa a wajen don yin tsaraba.
Sai dai ta ce a yanzu sun rasa dukkanin abubuwan biyu, inda ta ɗauko tukunyarsu ta girkin da kuma kaskon gas ɗin da suke amfani da shi a wajen, ta bar tashar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jirgin Ƙasa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA