Aminiya:
2025-09-18@00:41:51 GMT

An fara gyaran layin dogon Abuja-Kaduna bayan hatsarin jirgin ƙasa

Published: 29th, August 2025 GMT

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa ta Najeriya (NRC) ta fara aikin gyara layin dogon Abuja zuwa Kaduna da ya lalace sakamakon hatsarin jirgin kasa.

A ranar Talata da ta gabata ce jirgin mai tarago 10 da ya tashi da misalin karfe 11:00 na safe daga tasharsu da ke Kubwa a Abuja da nufin zuwa Kaduna, rikito daga kan hanyarsa a wata ƙaramar tasha da ke kauyen Asham, ’yan mintoci kalilan bayan fara tafiyar.

Hadimin Gwamnan Kano ya maka mawallafin Daily Nigerian a kotu saboda kiransa da ‘ɓarawo’ NAJERIYA A YAU: “Abin Da Ya Sa Muka Dawo Daga Rakiyar Kirifto”

Injin jirgin da kuma tarago biyu da ke biye masa sun samu mummunar illa, a yayin da ragowar taragu shida suka goce daga kan layin, sai kuma guda da ke daukar manyan mutane.

Wakilinmu da ya koma tashar jirgin ta Kubwa a ranar Alhamis, ya samu labarin cewa hukumar ta NRC ta bayar da aikin gyaran ne ga wani kamfanin ƙasar Sin wanda kuma ya fara aikin gyaran a ranar Laraba da ta gabata.

An dai kai taragu ukun ne zuwa babban tashar hukumar da ke yankin Idu a Abuja, a yayin da a ke saran ɗauko ragowar shidan da kuma injin jirgin a ranar ta Alhamis, kamar yadda majiyar ta bayyana.

Bayanan sun ce ana sa ran a fara gyaran ɓangaren layin dogon a ranar ta Alhamis bayan an kawar da ragowan taragun shida da a cewar majiyar ba za su iya tafiya da kansu ba har sai an ɗaga su a sakamakon lalacewar da suka yi.

A wani labarin kuma, yawancin ma’aikata da ke aiki a tashar jirgin ƙasan ta Kubwa, da sauran masu gudanar da ayyuka a wajen na ci gaba da hutun dole, lamarin da ya mayar da wajen tamkar na yanayin zaman makoki.

Wasu daga cikin ma’aikata ’yan ƙalilan da su ka leƙa wurin aiki a ranar, sun shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya fi shafar ma’aikata da ke ɓangaren sayar da tikitin jirgi, da masu aikin tsaftace wajen, da masu yin dako, sai kuma direbobin tasi, da dai sauransu.

Ɗaya daga cikin ma’aikatan da aka zanta da shi ya koka a kan yadda lamarin inda ya ce ya raba su da sana’arsu da kuma jefa su a cikin halin kunci.

Wata da ke aiki da kamfanin samar da abincin maƙulashe da ke raba dafaffiyar taliyar ga fasinjoji kyauta a duk ranakun Alhamis da Juma’a da kuma Asabar, ta ce ta je wajen a ranan tare da cikakken fatan an fara aiki.

Jami’ar mai suna Joy Ene Agu ta ce suna raba taliyar ne kamar katan huɗu a kowane yini cikin ranakun a matsayin dabarun tallata taliyarsu ga jama’a, sannan su sayar da ɗanyarta ga masu sha’awa a wajen don yin tsaraba.

Sai dai ta ce a yanzu sun rasa dukkanin abubuwan biyu, inda ta ɗauko tukunyarsu ta girkin da kuma kaskon gas ɗin da suke amfani da shi a wajen, ta bar tashar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jirgin Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.

Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.

Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin