Bincike Ya Nuna Tarin Fuka Na Kashe Mutum 71,000 A Nijeriya Duk Shekara
Published: 29th, August 2025 GMT
Duk da yawan wadanda aka gano suna dauke da cutar, jami’an kiwon lafiya sun bayyana irin ci gaban da ake samu. Daraktan kula da lafiyar al’umma a ma’aikatar lafiya ta tarayya, Dakta Godwin Ntadom, ya bayyana cewa; Nijeriya ta samu sanarwar bullar cutar tarin fuka mafi yawa a 2024, inda ta gano sama da mutum 400,000 da ke dauke da cutar, kwatankwacin kashi 79 cikin 100 na masu jinyar.
Haka nan, akwai yara da dama wadanda ke dauke da cutar ta TB, amma ba a gano ba. Kazalika, yaran da aka gano suna dauke da cutar, yawansu ya karu daga 8,293 a 2018 zuwa 43,000 a 2024, in ji shi.
Duk da haka, Ntadom ya bayyana cewa; tarin fuka wanda ba ya jin magani, shi ne wanda ya fi illa. “Adadin yawan masu dauke da cutar da ba a gano ba, su ne ke ci gaba da yada ta”, in ji shi.
Domin cike gibin da ake samu, gwamnatin tarayya a kwanan nan ta kaddamar da sauye-sauyen ayyukan fasaha. Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya sanar da tura na’urorin gwaji (D-ray) na wayar hannu guda 400 a fadin jihohin Nijeriya 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja.
“Wadannan rukunin, wadanda kwararru a bangaren ke sarrafa su, suna ba mu damar gano alamun cututtukan tarin fukar da ba a gano ba,” in ji Pate.
Gwamnati ta kuma damar yin gwajin kwayoyin cikin sauri. Tsakanin 2012 zuwa 2024, yawan kwararrun injinan gwaje-gwajen da aka samu sun karu daga 32 zuwa 513. Haka zalika, adadin cibiyoyin kula da tarin fuka ya kusan ninki biyu daga 12,606 a 2019, zuwa kusan 23,000 a 2024, wanda ya mamaye sama da rabin dukkanin cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: dauke da cutar
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
A ci gaba da wasannin neman shiga gasar cin kofin Nahiyyar Afirka na 2026 da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci, yanzu haka ƙasashe 6 sun samu nasarar shiga gasar.
Ƙasashen da suka samu tikitin sun haɗa da mai masaukin baƙi: Morocco da Najeriya da Zambia da Tanzania da Malawi da Algeria da Ghana da Senegal da Kenya da Burkina Faso da Cape Verde da Afrika ta Kudu.
Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29 ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu bayaWannan dai ita ce gasa karo na 14 da za a buga a tarihi daga ranar 17 ga watan Maris zuwa 3 ga watan Afrilu na 2026.
Ƙasashen da suka kai wasan kusa da na ƙarshe a Kofin Nahiyyar Afirkan za su wakilci nahiyar a Kofin duniya na mata da za a buga a ƙasar Brazil a 2027.