Ambaliya ta raba ƙauyukan Sakkwato 6 da sauran sassan jihar
Published: 29th, August 2025 GMT
Ambaliyar ruwar da ta biyo bayan mamakon ruwan saman da aka tafka ta raba kauyuka shida da ke karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sakkwato da saurann yankunan jihar.
Kauyukkan da ambaliyar ta shafa su ne Makuwana da Dangawo da Faru da Gumbula da ’Yan Faruna da kuma Magajin Dawaki, sannan ta lalata hanyar da ta hada kananan hukumomin Goronyo da Sabon Birni.
Tuni dai Majalisar Dokokin Jihar ta yi kira ga gwamnatin jiha da ta tarayya da ke kula da harkokin ruwa da su dauki matakin da ya dace kan wadanda lamarin ya shafa.
Hakan dai ya biyo bayan bukatar da dan Majalisar Dokokin Jihar mai wakiltar mazabar Sabon birni ta Kudu, Aminu Mustafa Boza, ya gabatar gaban majalisar kan bukatar tallafa wa yankunan da iftila’in ya shafa.
Boza a yayin zaman majalisar wanda mataimakin shugabanta, Alhaji Kabiru Ibrahim ya jagoranta ranar Alhamis, ya nemi ta jawo hankalin hukumomin da lamarin ya shafa kan halin da kauyukan suka ciki
Wani mazaunin daya daga cikin kauyukan, Sani Gumbula ya ce ruwan ya yi musu barna sosai don haka akwai bukatar gwamnati ta kawo musu agajin gaggawa.
“Yanzu abin da nake fada maka gidajenmu da yawa sun rushe, gonaki sun nutse a ruwa sanadin wannan iftila’i, mun yi asara matuka, muna kira ga gwamnati ta yi abin da ya dace a kankanen lokaci, gaskiya muna cikin damuwa,” in ji Sani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO) ya ƙaryata zargin da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya yi masa, dangane da mutuwar wasu marasa lafiya sakamakon katse wutar lantarki da aka ce kamfanin ya yi.
Asibitin na AKTH ya bayyana damuwarsa a ranar Lahadi kan abin da ya kira abin takaici yana mai cewa mutanen da suka mutu za su iya tsira da ransu da ba a ɗauke wutar ba.
Amma a martanin da ya bayar, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama’a na KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce asibitin na ƙoƙarin ɓata sunan kamfanin ne kawai, domin an dawo da wutar tun kafin asibitin ya fitar da wannan sanarwar.
Sani ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga wani yunƙurin da ake yi na raba ginin asibitin da cibiyoyin lafiya daga gidajen ma’aikatan asibitin.
“Cibiyar asibitin da cibiyoyin lafiya suna da alaƙa da layin 33kV na Zariya Road wanda aka fi ba fifiko wajen raba wuta, kuma suna samun kimanin sa’o’i 22 na wutar lantarki a kullum ƙarƙashin tsarin Band A.
“Amma, shugabannin AKTH sun dage cewa sai gidajen ma’aikata sun ci gaba da kasancewa a layin wutar lantarki ɗaya da cibiyoyin lafiya. Wannan ya janyo barazana ga inganci da kwanciyar hankali na wutar da aka ware wa asibitin.
“An yi ƙoƙari sau da dama don raba gidajen ma’aikata daga cibiyoyin lafiya, amma haƙarmu ba ta kai ga cimma ruwa ba saboda ƙin amincewar shugabannin asibitin. Abin takaici, wannan ya haifar da matsala mai tsanani da ta janyo katsewar wutar da muke ƙoƙarin kaucewa,” in ji KEDCO.
Don tabbatar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga asibitin, kamfanin KEDCO ya ce yana ci gaba da aikin raba layukan wutar lantarkin biyu. Ya ce annan mataki ya zama dole don tabbatar da inganci, tsaro da kyautata lantarki ga asibitin.
Kamfanin ya kuma zargi asibitin da rashin biyan kuɗin wutar lantarki da gidajen ma’aikata ke amfani da ita, wanda ke shafar ingancin ayyukan samar da wuta na kamfanin.
KEDCO ya ce a cikin wata wasiƙa da ya aike ranar 12 ga Agusta, 2025, Babban Jami’in Kasuwanci na kamfanin, Muhammad Aminu Ɗantata, ya sanar da Shugaban Asibitin AKTH game da shirin dakatar da samar da wutar lantarki ga gidajen ma’aikata da wuraren da ba su da muhimmanci, sakamakon rashin cikakken biyan kuɗin wutar wata-wata.
Wasiƙar ta bayyana cewa:
“Duk da roƙon da aka yi sau da dama, asibitin ya ƙi biyan cikakken kuɗin wutar da yake sha a duk wata.
Wannan ya haifar da bashin wutar lantarki da ya kai ₦949,880,922.45 a watan Agustan 2025.
“An bukaci asibitin ya biya kuɗin watan Agusta 2025 na ₦108,957,582.29 gaba ɗaya cikin kwanakin aiki 10, don kaucewa yanke wuta a wuraren da abin ya shafa,” in ji wasiƙar.
Kamfanin ya ƙuduri aniyar ci gaba da samar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga AKTH a matsayin babbar cibiyar lafiya.
A ƙarshe, KEDCO ya roƙi shugabannin asibitin da su ba da haɗin kai a aikin raba layukan wutar, wanda ya ce yana da amfani ga marasa lafiya, ma’aikata, da al’umma baki ɗaya.