Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na horar da matasa sana’o’i daban-daban a fadin kasar nan.

 

Sakataren Ma’aikatar Agaji da Rage Talauci, Dokta Yakubu Adam Kofar Mata, ya bayyana haka, a lokacin da ya kai ziyarar wayar da kan mahalarta shirin “Skill to Wealth” na shiyyar Arewa maso Yamma, wanda aka gudanar a Kano.

 

 

Dokta Kofar Mata ya jaddada cewa, makasudin bayar da horon shi ne don cika sabbin alkawurran da gwamnati mai ci ta dauka na karfafa matasa.

 

 

Shirin bayar da horon na da nufin wadata matasa sana’o’in da za su iya dogaro da kansu da kuma bayar da gudunmawa wajen ci gaban tattalin arzikin kasar.

 

 

Ko’odinetan shirin na Jiha Dokta Mahdi Isa ya bayyana cewa mahalarta taron 189 daga shiyyar Arewa maso Yamma suna samun horo kan aikin noma, gyaran injinan mota da sabunta makamashi.

 

 

Ya ce bayan kammala horon, za a baiwa mahalarta taron da kayayyakin fara kasuwanci domin su fara sana’o’insu.

 

 

An tsara shirin horarwa ne domin magance matsalar rashin aikin yi da fatara a tsakanin matasa a kasar.

 

Isa ya kara da cewa, ta hanyar koyon sana’o’i a bangarori daban-daban, za a ba wa mahalarta taron kwarin gwiwar zama ‘yan kasuwa da kuma ba da gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin kasa.

 

 

“Kwarin gwiwar da gwamnatin tarayya ta yi na karfafa wa matasa gwiwa ta hanyar koyon sana’o’i mataki ne mai kyau.

 

“Shirin horar da ”Skill to Wealth” wata shaida ce ga sabbin manufofin gwamnati, da ke da nufin inganta rayuwar ‘yan Najeriya, musamman matasa.”

 

 

Cover/Abdullahi jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro

Gwamnatin Jihar Yobe, ta sanar da rufe kasuwannin garuruwan Katarko, Kukareta da Buni Yadi saboda barazanar matsalar tsaro.

Wannan mataki na ɗaya daga cikin hanyoyin da gwamnatin ke ɗauka domin inganta tsaro a yankunan.

Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Sanarwar ta fito ne daga babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya).

Ya bayyana cewa an yanke wannan hukunci ne domin a samu damar gudanar da wasu ayyuka na musamman da suka shafi tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Ya ce wannan matakin na ɗan lokaci ne, kuma yana da nufin tabbatar da ci gaba da samun nasara a yaƙi da ‘yan ta’adda a jihar.

“Ko da yake hakan zai kawo ƙalubale ga al’umma, amma wajibi ne domin a cimma babban burin tsaro,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin na aiki tuƙuru don ganin an rage wa mutane raɗaɗin da wannan mataki zai haifar.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ba da haɗin kai da fahimta don a samu nasarar ayyukan tsaro da kuma wanzar da zaman lafiya gaba ɗaya a jihar.

Har ila yau, ya tabbatar wa al’umma cewa da zarar abubuwa sun daidaita, za a sake buɗe kasuwannin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
  • Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur
  • Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka
  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
  • Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Karamar Hukumar Maru Ta Bukaci A Dauki Matakan Kariya Kan Cutar Kwalaraci
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba