Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na horar da matasa sana’o’i daban-daban a fadin kasar nan.

 

Sakataren Ma’aikatar Agaji da Rage Talauci, Dokta Yakubu Adam Kofar Mata, ya bayyana haka, a lokacin da ya kai ziyarar wayar da kan mahalarta shirin “Skill to Wealth” na shiyyar Arewa maso Yamma, wanda aka gudanar a Kano.

 

 

Dokta Kofar Mata ya jaddada cewa, makasudin bayar da horon shi ne don cika sabbin alkawurran da gwamnati mai ci ta dauka na karfafa matasa.

 

 

Shirin bayar da horon na da nufin wadata matasa sana’o’in da za su iya dogaro da kansu da kuma bayar da gudunmawa wajen ci gaban tattalin arzikin kasar.

 

 

Ko’odinetan shirin na Jiha Dokta Mahdi Isa ya bayyana cewa mahalarta taron 189 daga shiyyar Arewa maso Yamma suna samun horo kan aikin noma, gyaran injinan mota da sabunta makamashi.

 

 

Ya ce bayan kammala horon, za a baiwa mahalarta taron da kayayyakin fara kasuwanci domin su fara sana’o’insu.

 

 

An tsara shirin horarwa ne domin magance matsalar rashin aikin yi da fatara a tsakanin matasa a kasar.

 

Isa ya kara da cewa, ta hanyar koyon sana’o’i a bangarori daban-daban, za a ba wa mahalarta taron kwarin gwiwar zama ‘yan kasuwa da kuma ba da gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin kasa.

 

 

“Kwarin gwiwar da gwamnatin tarayya ta yi na karfafa wa matasa gwiwa ta hanyar koyon sana’o’i mataki ne mai kyau.

 

“Shirin horar da ”Skill to Wealth” wata shaida ce ga sabbin manufofin gwamnati, da ke da nufin inganta rayuwar ‘yan Najeriya, musamman matasa.”

 

 

Cover/Abdullahi jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ba Ta Da Alkiblar Siyasa

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya bayyana cewa: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta da wani yanki na siyasa mai zaman kansa

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Yahudawan sahayoniya ba su da wata kafa ta siyasa mai cin gashin kanta, a maimakon haka dole ne a fahimci matsayinsu geopolitical bisa tsarin mulkin Amurka.

A jawabin da ya gabatar a wajen rufe taron tattaunawa na Tehran a jiya litinin, Qalibaf ya kara da cewa: A fagen siyasar kasa, siyasa ba ita ce kullin nauyi ba, a maimakon haka, labarin kasa shi ne ginshikin da siyasa ta ginu a kansa a matsayin wani mataki mai girma.

Ya bayyana cewa: Idan ana magana game da ababen more rayuwa da labarin ƙasa ke wakilta a zahiri, ana nufin nazarin abubuwa uku: Wuri, mutane da lokaci. Wato fahimtar nazarin al’amuran ɗan adam a lokuta daban-daban yana samuwa ne ta hanyar nazarin fifikon wuri. Don haka, a cikin binciken a fagen siyasa, za a dogara da wuri a matsayin tushen abubuwan more rayuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ba Ta Da Alkiblar Siyasa
  • Gwamnatin Kasar Masar Tana Shirye-Shiryen Sanya Kafar Wando Daya Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Isra’ila Ta Kai Hari Ga Rumbun Magungunna A Kudancin Gaza
  • Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu
  • Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin  
  • Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20
  • Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)