HausaTv:
2025-08-04@10:44:41 GMT

 Kotun Duniya Ta Wanke HDL Akan Zargin Kisan Kiyashi A Sudan

Published: 5th, May 2025 GMT

Kotun duniya ta yi watsi da karar da Sudan ta kai Hadaddiyar Daular Larabawa tana mai zarginta da hannu a kisan kiyashin da aka yi wa al’ummar wannan kasa.

A yau Litinin ne kotun duniyar ta yi watsi da karar ta Sudan, tana mai wanke Hadaddiyar Daular Larabawa.

Ita dai Sudan ta zargi Hadaddiyar Daular Larabawar da cewa ta hada baki da dakarun kai daukin gaggaawa wajen yi wa mutanen yankin Darfur kisan kiyashi.

A nata gefen Hadaddiyar Daular Larabawan ta ki amincewa da tuhumar da Sudan ta yi mata  tana mai siffata ta da cewa; Farfaganda ce, kuma Sudan din ta yi hakan ne domin kawar da hankulan duniya daga kan laifukan da sojoji suke aikatawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Hadaddiyar Daular

এছাড়াও পড়ুন:

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Wani fim mai suna “Dead to Rights”, wanda aka shirya game da kisan kiyashin da aka yi a birnin Nanjing, ya mamaye kasuwar fina-finai ta lokacin zafi ta kasar Sin, inda kudin shigar da aka samu da shi ya zarce yuan biliyan daya, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 140 cikin kwanaki takwas kacal.

Wanda aka yi amfani da ingantattun shaidun hotuna na ta’asar yakin da Japanawa suka aikata a lokacin kisan kiyashin Nanjing, Fim din na “Dead to Rights” ya ba da labari ne na wani rukunin fararen hula na kasar Sin da suka nemi mafaka a dakin daukar hoto a lokacin muguwar mamayar da azzaluman Japanawa suka yi a birnin Nanjing.

A wani yunkuri na neman tsira da rayukansu hajaran-majaran, an tilasta musu taimaka wa wani mai daukar hoto na sojan Japan wajen wanke hotuna, amma kwatsam suka gano dodon hotunan yana dauke da shaidun munanan ta’asar da sojojin Japan suka tafka a sassan birnin. Bisa kudirinsu na tona asirin abin da ya faru, sai suka boye dodon hotunan tare da jefa rayuwarsu cikin hadari wajen bayyana su ga duniya.

Bisa kididdigar da aka yi na baya-bayan nan, ana sa ran “Dead to Rights” zai samu kudin shiga fiye da yuan biliyan 4, inda aka samu karin kiyasin da aka yi a baya. Idan har aka cimma burin hakan, zai zama fim na biyu mafi samun tagomashi a kasar Sin a bana, inda ya biyo bayan fim din “cartoon” na “Ne Zha 2.” (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD ta yi gargadi  game da mummunar matsalar da yunwa ka iya haifarwa ga al’ummar Gaza
  • Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi
  • Jamus ta soma jefa kayan agaji a Zirin Gaza
  • Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
  • Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka
  • ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar
  • Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu