An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
Published: 17th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.
Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.
Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.
Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.
Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.
“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”
Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.
A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.
Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.
Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.
Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.
Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.
Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo
এছাড়াও পড়ুন:
Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
Ya ce: “Ba mu kai inda muke so ba a fannin tattalin arziki, amma muna iya gani cewa abubuwa suna tafiya a hankali. Shugaban Ƙasa ya faɗa sau da dama cewa mun fara fitowa daga ƙunci.
“Na san mutane da yawa za su ce ba mu kai ga cikakken cigaba da jin daɗin tattalin arziki ba tukuna. Gaskiya ne! Ni ma na yarda. Amma ba za mu ce babu cigaba ko kaɗan ba.”
Ya ƙara da cewa: “Ko hukumomin ƙididdiga na duniya suna fara ba Nijeriya kyakykyawan matsayi. Muna ganin alamu na ɗagawa a hanyar da ake tafiyar da tattalin arzikin mu.”
Idris ya ce manyan matakan sauyi kamar cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar kuɗi suna fara nuna tasiri mai kyau a ƙasar nan.
Haka kuma ya bayyana cewa sama da ɗalibai 300,000 ne suke cin gajiyar shirin bayar da rancen karatu na gwamnati, wanda ke ɗaukar nauyin kuɗin makaranta da kuma ciyar da su.
Ya ce: “Saboda wannan manufa da aka tsara ta gwamnati, sama da ɗalibai 300,000 na Nijeriya da a da ba za su iya zuwa makaranta ba ko kuma da suka riga suka bar makaranta, yanzu suna da damar komawa makaranta domin gwamnati tana biya masu kuɗin makaranta da na ciyarwa. Ba a taɓa samun irin wannan ba.”
A kan batun tsaro, Ministan ya ce gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi don shawo kan matsalolin tsaro, inda ya ce dakarun soji na samun nasarori a yaƙi da masu laifi a sassa daban-daban na ƙasar nan.
Ya roƙi kafafen yaɗa labarai da su goyi bayan ƙoƙarin da rundunonin tsaro suke yi, tare da guje wa bai wa masu laifi muhimmanci fiye da kima.
“Ina ta faɗa tun da farko cewa ba daidai ba ne mu a matsayin mu na ‘yan jarida mu riƙa ba waɗannan masu laifi, masu tayar da ƙayar baya, ‘yan ta’adda ko ɓarayi ko duk yadda za a kira su, fifiko fiye da ‘yan Nijeriya nagari,” inji shi.
Ya ce ya kamata kafafen watsa labarai su riƙa bayyana nasarorin da sojoji suke samu da sadaukarwar su, maimakon maida hankali kawai a kan hare-hare da rashin nasara.
Idris ya bayyana cewa ko da yake aikin kafafen watsa labarai ne su riƙa sa ido kan gwamnati ta hanyar suka mai amfani, wajibi ne su kuma riƙa bayyana nasarori da cigaban da ake samu.
A martanin sa kan Rahoton Gyaran Dokoki da ƙungiyar ta gabatar, Ministan ya ce zai tattauna da Ministan Shari’a kuma babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, tare da kafa kwamitin musamman a ma’aikatar sa domin nazarin rahoton.
Ya jaddada cewa manufar gwamnatin Tinubu tana daga cikin ginshiƙan dimokiraɗiyya ita ce kare ‘yancin faɗar albarkacin baki da ‘yancin kafafen yaɗa labarai.
Sai dai ya ja hankalin ‘yan jarida da su riƙa amfani da wannan ‘yanci cikin kishi da kishin ƙasa, tare da riƙon gaskiya da haɗin kai don ci gaban ƙasa.
Idris ya taya sababbin shugabannin ƙungiyar murna, tare da bayyana shirin sa na ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnati da kafafen watsa labarai.
Tun da farko a jawabin sa, Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Editocin Nijeriya, Dakta Sebastian Abu, ya bayyana cewa tawagar ta kai ziyara ofishin Ministan ne don gabatar da rahoton Kwamitin Sauya Dokokin Ƙungiyar a hukumance.
Ya bayyana cewa rahoton ya nuna wasu tsofaffin dokoki a kundin tsarin mulki da suka zama ƙalubale ga ‘yancin aikin jarida a Nijeriya, waɗanda ya dace a duba ko a cire su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp