Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
Published: 13th, April 2025 GMT
Wani matashi ɗan shekara 18 mai suna Bakura Muhammed, ya gamu da ajalinsa a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ƙungiyoyin matasa masu gaba da juna da ake wa laƙabi da Malians a Maiduguri.
Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zaga-zola Makama cewa, rikicin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar 4 ga watan Afrilun nan a yankin Ajari da Tashar Lara, inda matasan ɓangarorin biyu suka yi artabu da juna.
An daɓa wa wanda aka kashen wuƙa a ciki, wanda ba tare da ɓata lokaci ba jami’an tsaro na Maidugurin suka ɗauke shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwarsa.
Wata majiyar ‘yan sanda ta ce, an kama wasu mutane bakwai masu shekaru tsakanin 15 zuwa 24.
Majiyar ta bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Ba’abba Kyari mai kimanin shekara 20 sai Ali Alhaji Goni Ali dan shekara 20 da Muhammed Audu mai kimanin shekara 18, sai Ali Isa mai shekara 15 da Adam Sabir mai shekara 15 da Mohammed Tujja shekaru 17 da Usman Kasim dan shekara 24
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Borno Ƙungiyar Asiri
এছাড়াও পড়ুন:
Malaman firamare sun janye yajin aiki a Abuja
Malaman makarantun firamare da ke ƙarƙashin Hukumar Ilimin Ƙananan Hukumomi (LEA) a babban birnin tarayya Abuja sun janye yajin aikin da suka tsunduma watanni uku da suka gabata.
Ana iya tuna cewa, tun a watan Maris ne dai malaman da ke ƙarƙashin ƙungiyar malamai ta ƙasa NUT suka tsunduma yajin aikin kan abin da suka kira rashin byan haƙƙoƙinsu na mafi ƙarancin albashi da aka ƙayyade na Naira dubu 70.
An kama ɓarayin babura a Gombe An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a NijeriyaAminiya ta ruwaito cewa, a ranar Alhamis din makon jiya ce Ministan Abuja, Nyesome Wike ya gana da shugabannin ƙungiyar malaman daga ƙananan hukomomi shida na Abuja da wasu masu ruwa da tsaki.
Bayan wannan ganawar ce gamayyar ƙungiyoyin malaman a yammacin wannan Talatar ta sanar da janye yajin aikin wanda ta ce zai fara ne daga gobe Laraba, 9 ga watan Yulin 2025.
Shugabannin ƙungiyoyin malaman da suka sanya hannu a takardar janye yajin aikin sun bayyana cimma wannan matsaya ce bayan sakin wani kaso da ya kai kusan naira biliyan 16 na bashin da za a biya malaman albashinsu na watannin da aka dokar sabon mafi ƙarancin albashin ta soma aiki.
Sanarwar ta ambato ƙungiyar malaman tana yi wa mambobinta godiya bisa haƙuri da jajircewa da kuma hadin kan da suka bayar tsawon lokacin da aka shafa ana yajin aikin.
Haka kuma, ƙungiyoyin malaman sun miƙa godiya ta musamman zuwa hedikwatar ƙungiyar malamai ta ƙasa NUT da ƙungiyar ƙwadago NLC reshen Abuja, da sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin fararen hula da duk wadanda suka tsaya tsayin daka wajen ganin gwamnati ta waiwayi buƙatunsu.