Aminiya:
2025-06-22@17:53:20 GMT

Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri

Published: 13th, April 2025 GMT

Wani matashi ɗan shekara 18 mai suna Bakura Muhammed, ya gamu da ajalinsa a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ƙungiyoyin matasa masu gaba da juna da ake wa laƙabi da Malians a Maiduguri.

Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zaga-zola Makama cewa, rikicin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar 4 ga watan Afrilun nan a yankin Ajari da Tashar Lara, inda matasan ɓangarorin biyu suka yi artabu da juna.

An daɓa wa wanda aka kashen wuƙa a ciki, wanda ba tare da ɓata lokaci ba jami’an tsaro na Maidugurin suka ɗauke shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwarsa.

Wata majiyar ‘yan sanda ta ce, an kama wasu mutane bakwai masu shekaru tsakanin 15 zuwa 24.

Majiyar ta bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Ba’abba Kyari mai kimanin shekara 20 sai Ali Alhaji Goni Ali dan shekara 20 da Muhammed Audu mai kimanin shekara 18, sai Ali Isa mai shekara 15 da Adam Sabir mai shekara 15 da Mohammed Tujja shekaru 17 da Usman Kasim dan shekara 24

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno Ƙungiyar Asiri

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

A nasu ɓangaren, ƙungiyar kare haƙƙin Musulmi, MURIC, ta gargaɗi APC da Shugaba Tinubu da kada su sauya Shettima a matsayin mataimaki a 2027.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce duk wani yunkuri na cire Shettima zai zama matakin da bai dace ba kuma ya kamata a nemi shawara daga manyan masu ruwa da tsaki kafin ɗaukar kowanne mataki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos