Sudan ta kai karar Hadaddiyar Daular Larabawa a Kotun ICJ
Published: 10th, April 2025 GMT
Jakadan Sudan a Tehran, Abdul Aziz Hassan Saleh, ya tabbatar da cewa, za a gudanar da zaman farko na kotun kasa da kasa da ke birnin Hague a yau Alhamis, domin duba korafin da Sudan ta shigar kan kasar Hadaddiyar Daular Larabawa, kan rawar da take takawa a yakin da ake ci gaba da yi a kasar, da kuma goyon bayan da take baiwa mayakan sa kai na Rapid Support Forces, tana mai kallonta a matsayin wani bangare na haddasa rikicin da ke faruwa a Sudan.
A wani taron manema labarai da ya gudanar a wannan Laraba 9 ga watan Afrilu a ofishin jakadancin Sudan da ke Tehran, jakadan Sudan ya yi tsokaci kan laifukan da dakarun RSF suka aikata a jihar Khartoum, inda ya jaddada faruwar munanan laifuka kan fararen hula, da suka hada da kama mutane ba bisa ka’ida ba, da take hakkin fursunoni, da amfani da yunwa a matsayin makami, da kuma cin zarafin mata.
Jakadan ya yi nuni da cewa, ya zuwa yanzu sojojin Sudan sun kubutar da fursunoni kusan 4,700 da aka sace daga gidajensu, an tsare su ne cikin yanayi na rashin mutuntaka, inda gidajen yari ba su da ko da abubuwan more rayuwa.
Ya kara da cewa, “Rundunar RSF ba su bi ka’idojin shari’a ba wajen mu’amala da fursunoni, a maimakon haka, sun aikata munanan laifuka, har ma a kan kananan yara, ta hanyar yin garkuwa da su tilasta musu ficewa daga gidajensu har ma da karbar kudi daga hannunsu.
Ya kuma yi bayanin cewa har yanzu sojojin Sudan ba su samu damar shiga dukkan wuraren da dakarun RSF ke rike da fararen hula ba, inda ya ce an sace mata da ‘yan mata akalla 200 tare da kai su wuraren da ba a sani ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Leroy Sane ya koma Galatasaray
Kungiyar kwallon kafa ta Galatasaray a wannan Alhamis din ta sanar da daukar dan wasan Jamus, Leroy Sane daga Bayern Munich.
Kungiyar ta Turkiyya ta dauki dan wasan ne kyauta bayan kwantaraginsa ya kare a Munich.
Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – ManeSane mai shekaru 29 ya rattaba hannu kan kwantaragin shekaru uku inda zai rika daukar albashin Yuro miliyan 9 — kwantankwacin Dala miliyan 10.4 — duk shekara kamar yadda kulob din bayyana.
Sane ya buga wa kasarsa ta Jamus wasanni 70, inda kuma ya lashe kofunan Bundesliga guda hudu a Bayern Munich tun bayan raba gari da Manchester City, inda ya dauki Firimiyar Ingila guda biyu.A kakar bana Sane ya jefa kwallaye 13 a duk gasannin da ya haska, inda ya taimaka wa Bayern lashe gasar Bundesliga bayan ta subuce daga hannunta a kakar bara.
AFP